Jam’iyyar adawa ta ADC ta bayyana rashin gamsuwarta kan yadda gwamnatin APC ke amfani da hukumar yaki da cin hanci da rashawa da kuma hukumomin tsaro wajen farautar ‘yan adawa a kasar nan.
Jam’iyyar ta ce irin wannan mataki ba zai haifar da sahihin zabe mai cike da adalci ba a 2027 da kuma yi wa tsarin shari’a karen-tsaye.
- Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Tiriliyan ₦4.4 Na Shekarar 2026
- Jam’iyyar APC Ta Ribas Ta Yi Watsi Da Matakin Tsige Gwamna Fubara
Bayanin hakan ya fito ne daga bakin Mataimakin Shugaban Jam’iyyar ADC na kasa, Malam Jafaru Sani, a wata hira da ya yi da wakilinmu a Kaduna.
Malam Jafaru ya bayyana cewa jam’iyyar ADC ba ta goyon bayan cin hanci da rashawa ko aikata laifuka ta kowace hanya, sai dai ya jaddada cewa wajibi ne a bi tsarin shari’a yadda ya kamata wajen hukunta duk wanda aka samu ya aikata laifi ba tare da nuna bangaranci ko amfani da karfin gwamnati wajen gallaza wa ‘yan adawa ba.
Ya zargi gwamnatin jam’iyyar APC da amfani da hukumomin tsaro da na yaki da cin hanci da rashawa wajen musgunawa da tsoratar da ‘yan adawa, lamarin da ya ce na iya kawo cikas ga dimokuradiyya da adalci a kasar nan.
A cewarsa, ADC na da kudirin aiwatar da gyare-gyare masu ma’ana a bangaren shari’a domin tabbatar da ‘yancin kai, gaskiya da adalci ga kowa, tare da hana amfani da hukumomi wajen cimma muradun siyasa.
Ya kara da cewa jam’iyyar ADC na kira ga ‘yan Nijeriya da su tsaya tsayin daka wajen kare dimokuradiyya da tabbatar da cewa ana gudanar da siyasa bisa gaskiya, adalci da bin doka da oda.
Da yake bayani dangane da harkokin tsaro, shugaban ya bayyana kudirin jamiyyar ADC na magance matsalar rashin tsaro da ke addabar yankin Arewacin kasar nan idan har ta samu damar rike madafun iko a zabukan 2027 masu zuwa.















Discussion about this post