ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Ya Garzaya EFCC Da Ƙarar Tsohon Shugaban NMDPRA Bayan Janye Ta Daga ICPC

by Abubakar Sulaiman
6 months ago
Dangote

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ta hannun lauyoyinsa, ya shigar da wata sabuwar ƙara a gaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Ƙasa (EFCC) kan tsohon Babban Daraktan Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur (NMDPRA), Farouk Ahmed.

Wannan ci gaban ya tabbata ne cikin wata sanarwa da sashin yaɗa labaran Kamfanin Dangote ya fitar a ranar Juma’a. A baya, Dangote ya kai ƙara ga Hukumar ICPC inda ya zargi Farouk Ahmed da kashe kimanin dala miliyan 5 wajen karatun ’ya’yansa a makarantar sakandare a ƙasar Switzerland. Duk da cewa Dangote ya janye ƙarar kwanaki kaɗan da suka wuce, ICPC ta bayyana cewa za ta ci gaba da bincike kan lamarin.

  • Har Yanzu Ana Yi Wa Matatar Man Mu Bita Da Ƙulli – Dangote
  • Ƙungiyar Kwankwaso National Network Ta Gudanar Da Taron Kudu Maso Yamma A Ibadan

Sanarwar ta ce yanke shawarar kai ƙarar zuwa EFCC ya biyo bayan “janye ƙarar daga ICPC a matsayin dabara domin hanzarta tsarin gurfanarwa da shari’a.” A cikin ƙarar da aka miƙa wa EFCC, Dangote ya nemi a binciki zargin cin zarafin ofis da kuma tara dukiya ta haramtacciyar hanya da ake yi wa Farouk Ahmed.

ADVERTISEMENT

Ƙarar, wadda babban lauyan Dangote, Dokta O.J. Onoja ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa Dangote a shirye yake ya gabatar da hujjoji masu ƙarfi domin tabbatar da zargin almundahana da rashin barnar kuɗi da ake yi wa tsohon shugaban NMDPRA. Har ila yau, an jaddada cewa EFCC na da cikakken ikon bincike da gurfanar da masu laifin cin hanci da rashawa.

Lauyan ya kuma yi kira ga EFCC ƙarƙashin jagorancin shugabanta, Mista Olanipekun Olukoyede, da ta gudanar da cikakken bincike kan zargin, tare da tabbatar da gurfanar da Ahmed gaban shari’a idan aka same shi da laifi, domin nuna cewa babu wanda ya fi ƙarfi a gaban doka.

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

Dangote
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
  • Abubakar Sulaiman
    TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV
  • Abubakar Sulaiman
    DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

MASU ALAKA

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Ta’addanci
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Next Post
Yerima Shettima Ya Gudanar Da Aikin Duba Lafiya Kyauta Ga Mutane 500 A Kaduna

Yerima Shettima Ya Gudanar Da Aikin Duba Lafiya Kyauta Ga Mutane 500 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026
Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

July 9, 2026
‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

July 9, 2026
Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

July 9, 2026
Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

July 9, 2026
Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

July 9, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

July 9, 2026
An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

July 9, 2026
kebbi

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.