Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ta hannun lauyoyinsa, ya shigar da wata sabuwar ƙara a gaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Ƙasa (EFCC) kan tsohon Babban Daraktan Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur (NMDPRA), Farouk Ahmed.
Wannan ci gaban ya tabbata ne cikin wata sanarwa da sashin yaɗa labaran Kamfanin Dangote ya fitar a ranar Juma’a. A baya, Dangote ya kai ƙara ga Hukumar ICPC inda ya zargi Farouk Ahmed da kashe kimanin dala miliyan 5 wajen karatun ’ya’yansa a makarantar sakandare a ƙasar Switzerland. Duk da cewa Dangote ya janye ƙarar kwanaki kaɗan da suka wuce, ICPC ta bayyana cewa za ta ci gaba da bincike kan lamarin.
- Har Yanzu Ana Yi Wa Matatar Man Mu Bita Da Ƙulli – Dangote
- Ƙungiyar Kwankwaso National Network Ta Gudanar Da Taron Kudu Maso Yamma A Ibadan
Sanarwar ta ce yanke shawarar kai ƙarar zuwa EFCC ya biyo bayan “janye ƙarar daga ICPC a matsayin dabara domin hanzarta tsarin gurfanarwa da shari’a.” A cikin ƙarar da aka miƙa wa EFCC, Dangote ya nemi a binciki zargin cin zarafin ofis da kuma tara dukiya ta haramtacciyar hanya da ake yi wa Farouk Ahmed.
Ƙarar, wadda babban lauyan Dangote, Dokta O.J. Onoja ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa Dangote a shirye yake ya gabatar da hujjoji masu ƙarfi domin tabbatar da zargin almundahana da rashin barnar kuɗi da ake yi wa tsohon shugaban NMDPRA. Har ila yau, an jaddada cewa EFCC na da cikakken ikon bincike da gurfanar da masu laifin cin hanci da rashawa.
Lauyan ya kuma yi kira ga EFCC ƙarƙashin jagorancin shugabanta, Mista Olanipekun Olukoyede, da ta gudanar da cikakken bincike kan zargin, tare da tabbatar da gurfanar da Ahmed gaban shari’a idan aka same shi da laifi, domin nuna cewa babu wanda ya fi ƙarfi a gaban doka.















Discussion about this post