ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Ta Yi Fatali Da Sabon Jadawalin Zaɓe Da INEC Ta Fitar

by Yusuf Shuaibu
6 months ago
ADC

Jam’iyyar ADC ta yi fatali da sabon jadawalin zaɓe da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta fitar, tana iƙirarin cewa an tsara shi ne don ware jam’iyyun adawa kafin zaɓen 2027.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya sanya hannu, jam’iyyar ta ce jadawalin da aka sake tsarawa ba kawai shirin gudanarwa ba ne, wani tuggun siyasa ne da rai raunana ƴan adawa.

ADC ta yi iƙirarin cewa sabbin abubuwan da aka ƙaƙaba a cikin dokar zaɓe ta 2026 sun yi wa jam’iyyun adawa sauri yawa.

ADVERTISEMENT

A cewar sabon jadawalin zaɓeni, za a gudanar da zaɓen fitar da gwani na jam’iyyu tsakanin 23 ga Afrilu da 30 ga Mayu, 2026. Duk da haka, jam’iyyu dole ne su miƙa cikakken rajistar mambobinsu ta na’urar zamani ga INEC kafin ranar 2 ga Afrilu, 2026, makonni kaɗan masu zuwa.

Jam’iyyar ta nuna cewa sashe na 77 na dokar, wanda ke cewa kowace jam’iyya da ta kasa gabatar da rajistar mambobinta akan lokaci, ba za ta gabatar da ɗan takara a wannan zaɓe ba. ADC ta bayyana wannan lamarin a matsayin wanda ya saɓa wa doka wacce aka saɓa.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

“Wannan ba dokokin cikin gida ba ne. An ƙirƙiresu ne da gangan don sanya shinge ga ‘yan adawa daga shiga zaɓen da ke tafe,” in ji sanarwar.

ADC ta bayyana cewa jam’iyyar mai mulki ta riga ta fara tattara irin wannan rajista tun daga watan Fabrairu 2025, kafin ta samar da dokar, wanda ya ba ta babbar dama.

Ta ƙara da cewa yayin da jam’iyyar mai mulki ta kwashe kusan shekara guda tana yin shiri, ana sa ran sauran jam’iyyun adawa su kammala wannan tsari a kusan wata guda. ADC ta bayyana wannan a matsayin abin da ba zai yiwu ba a aikace.

Jam’iyyar ta kuma zargi cewa tasirin sabon jadawalin da dokar zaɓe sun bayyana Ƙarara cewa Shugaban ƙasa, Bola Tinubu ake share wa hanya don ya yi tazarce a zaɓen 2027.

Ya yi kira ga ƙungiyoyin fararen hula da ɗaukacin ‘yan Nijeriya daga ɓangarorin siyasa daban-daban su duba wannan jadawalin tare da haɗa kai da su wajen neman adalci. Ta yi gargaɗin cewa dimokuraɗiyya ba za ta iya wanzuwa ba idan an shamfiɗa dokoki don fifita wani ɓangare guda ɗaya.

 

ADC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Matasa A Jihar Nasarawa Sun Buƙaci Gwamnati Ta Inganta Wutar Lantarki

Matasa A Jihar Nasarawa Sun Buƙaci Gwamnati Ta Inganta Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.