ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Ta Yi Fatali Da Sabon Jadawalin Zaɓe Da INEC Ta Fitar

by Yusuf Shuaibu
4 months ago
ADC

Jam’iyyar ADC ta yi fatali da sabon jadawalin zaɓe da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta fitar, tana iƙirarin cewa an tsara shi ne don ware jam’iyyun adawa kafin zaɓen 2027.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya sanya hannu, jam’iyyar ta ce jadawalin da aka sake tsarawa ba kawai shirin gudanarwa ba ne, wani tuggun siyasa ne da rai raunana ƴan adawa.

ADC ta yi iƙirarin cewa sabbin abubuwan da aka ƙaƙaba a cikin dokar zaɓe ta 2026 sun yi wa jam’iyyun adawa sauri yawa.

ADVERTISEMENT

A cewar sabon jadawalin zaɓeni, za a gudanar da zaɓen fitar da gwani na jam’iyyu tsakanin 23 ga Afrilu da 30 ga Mayu, 2026. Duk da haka, jam’iyyu dole ne su miƙa cikakken rajistar mambobinsu ta na’urar zamani ga INEC kafin ranar 2 ga Afrilu, 2026, makonni kaɗan masu zuwa.

Jam’iyyar ta nuna cewa sashe na 77 na dokar, wanda ke cewa kowace jam’iyya da ta kasa gabatar da rajistar mambobinta akan lokaci, ba za ta gabatar da ɗan takara a wannan zaɓe ba. ADC ta bayyana wannan lamarin a matsayin wanda ya saɓa wa doka wacce aka saɓa.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

“Wannan ba dokokin cikin gida ba ne. An ƙirƙiresu ne da gangan don sanya shinge ga ‘yan adawa daga shiga zaɓen da ke tafe,” in ji sanarwar.

ADC ta bayyana cewa jam’iyyar mai mulki ta riga ta fara tattara irin wannan rajista tun daga watan Fabrairu 2025, kafin ta samar da dokar, wanda ya ba ta babbar dama.

Ta ƙara da cewa yayin da jam’iyyar mai mulki ta kwashe kusan shekara guda tana yin shiri, ana sa ran sauran jam’iyyun adawa su kammala wannan tsari a kusan wata guda. ADC ta bayyana wannan a matsayin abin da ba zai yiwu ba a aikace.

Jam’iyyar ta kuma zargi cewa tasirin sabon jadawalin da dokar zaɓe sun bayyana Ƙarara cewa Shugaban ƙasa, Bola Tinubu ake share wa hanya don ya yi tazarce a zaɓen 2027.

Ya yi kira ga ƙungiyoyin fararen hula da ɗaukacin ‘yan Nijeriya daga ɓangarorin siyasa daban-daban su duba wannan jadawalin tare da haɗa kai da su wajen neman adalci. Ta yi gargaɗin cewa dimokuraɗiyya ba za ta iya wanzuwa ba idan an shamfiɗa dokoki don fifita wani ɓangare guda ɗaya.

 

ADC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Matasa A Jihar Nasarawa Sun Buƙaci Gwamnati Ta Inganta Wutar Lantarki

Matasa A Jihar Nasarawa Sun Buƙaci Gwamnati Ta Inganta Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026
Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

July 13, 2026
Majalisar Gudanarwa Ta Sin Ta Wallafa “Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Kan Kiyaye Lafiyar Al’ummar Kasar”

Majalisar Gudanarwa Ta Sin Ta Wallafa “Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Kan Kiyaye Lafiyar Al’ummar Kasar”

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.