ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Ta Yi Fatali Da Sabon Jadawalin Zaɓe Da INEC Ta Fitar

by Yusuf Shuaibu
4 months ago
ADC

Jam’iyyar ADC ta yi fatali da sabon jadawalin zaɓe da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta fitar, tana iƙirarin cewa an tsara shi ne don ware jam’iyyun adawa kafin zaɓen 2027.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya sanya hannu, jam’iyyar ta ce jadawalin da aka sake tsarawa ba kawai shirin gudanarwa ba ne, wani tuggun siyasa ne da rai raunana ƴan adawa.

ADC ta yi iƙirarin cewa sabbin abubuwan da aka ƙaƙaba a cikin dokar zaɓe ta 2026 sun yi wa jam’iyyun adawa sauri yawa.

ADVERTISEMENT

A cewar sabon jadawalin zaɓeni, za a gudanar da zaɓen fitar da gwani na jam’iyyu tsakanin 23 ga Afrilu da 30 ga Mayu, 2026. Duk da haka, jam’iyyu dole ne su miƙa cikakken rajistar mambobinsu ta na’urar zamani ga INEC kafin ranar 2 ga Afrilu, 2026, makonni kaɗan masu zuwa.

Jam’iyyar ta nuna cewa sashe na 77 na dokar, wanda ke cewa kowace jam’iyya da ta kasa gabatar da rajistar mambobinta akan lokaci, ba za ta gabatar da ɗan takara a wannan zaɓe ba. ADC ta bayyana wannan lamarin a matsayin wanda ya saɓa wa doka wacce aka saɓa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Wannan ba dokokin cikin gida ba ne. An ƙirƙiresu ne da gangan don sanya shinge ga ‘yan adawa daga shiga zaɓen da ke tafe,” in ji sanarwar.

ADC ta bayyana cewa jam’iyyar mai mulki ta riga ta fara tattara irin wannan rajista tun daga watan Fabrairu 2025, kafin ta samar da dokar, wanda ya ba ta babbar dama.

Ta ƙara da cewa yayin da jam’iyyar mai mulki ta kwashe kusan shekara guda tana yin shiri, ana sa ran sauran jam’iyyun adawa su kammala wannan tsari a kusan wata guda. ADC ta bayyana wannan a matsayin abin da ba zai yiwu ba a aikace.

Jam’iyyar ta kuma zargi cewa tasirin sabon jadawalin da dokar zaɓe sun bayyana Ƙarara cewa Shugaban ƙasa, Bola Tinubu ake share wa hanya don ya yi tazarce a zaɓen 2027.

Ya yi kira ga ƙungiyoyin fararen hula da ɗaukacin ‘yan Nijeriya daga ɓangarorin siyasa daban-daban su duba wannan jadawalin tare da haɗa kai da su wajen neman adalci. Ta yi gargaɗin cewa dimokuraɗiyya ba za ta iya wanzuwa ba idan an shamfiɗa dokoki don fifita wani ɓangare guda ɗaya.

 

ADC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Matasa A Jihar Nasarawa Sun Buƙaci Gwamnati Ta Inganta Wutar Lantarki

Matasa A Jihar Nasarawa Sun Buƙaci Gwamnati Ta Inganta Wutar Lantarki

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.