Ƙungiyar Al-Qadsiah ta Saudiyya ta fara tattaunawa da FC Porto ta Portugal kan yiwuwar ɗaukar ɗan wasan bayan Nijeriya, Zaidu Sanusi, wanda ya shiga shekarar ƙarshe ta kwantiraginsa da ƙungiyar. Rahotanni sun ce Zaidu, mai shekaru 29, bai cimma yarjejeniya da Porto kan sabunta kwantiraginsa na shekaru biyu ba, musamman saboda batun karin albashin da ya nema.
Saboda rashin cimma matsaya kan sabon kwantiragi, ana ganin Porto na iya sayar da ɗan wasan a wannan kakar domin kauce wa barin sa ya tafi kyauta idan kwantiraginsa ya ƙare.
Jami’an Al-Qadsiah sun riga sun gudanar da tattaunawa ta farko da shugabannin Porto, inda ƙungiyar ta Portugal ta sanya Yuro miliyan 10 a matsayin kuɗin da za ta amince da shi domin sallamar ɗan wasan.
Zaidu ya koma FC Porto ne daga Santa Clara a watan Agustan 2020, inda ya zama ɗaya daga cikin ‘yan wasan da suka taka muhimmiyar rawa a ƙungiyar. A tsawon zamansa a Porto, ɗan wasan ya lashe kofuna takwas, ciki har da gasar Primeira Liga da Taça de Portugal.
Baya ga Al-Qadsiah, Zaidu ya kuma jawo hankalin wasu ƙungiyoyin Turai, ciki har da Atalanta ta Italiya da Leeds United ta Ingila. Sai dai komawarsa Saudiyya na iya zama zaɓin da zai ba shi damar samun albashi mai tsoka, yayin da Porto kuma za ta samu damar samun kuɗin sayar da shi kafin kwantiraginsa ya ƙare.














