ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanya Dokar Ta -Ɓaci Kan Tsaro Bai Da Amfani – Datti Baba-Ahmed

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Baba

LABARAI MASU NASABA

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

Tsohon ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour a zaɓen 2023, Yusuf Datti Baba-Ahmed, ya soki matakin Shugaba Bola Tinubu na ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro a faɗin ƙasa, yana mai cewa matakin bai dace ba kuma ba shi ne muhimmin abin da ke magance matsalar tsaro ba.

A hirarsa da Arise TV, Baba-Ahmed ya ce dokar ta-ɓacin da aka sanar ta samo asali ne daga rashin fahimtar ainihin matsalar da ake fuskanta, yana mai bayyana ta a matsayin abin ban dariya da ba zai kawo sauyi ba.

  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Baba-Ahmed ya yi tir da shawarar gwamnatin tarayya ta dakatar da gina makarantu a yankunan karkara saboda barazanar hare-hare, idan ya bayyana wannan shawara “mai haɗari kuma babban kuskure.” Ya ce yaƙin da malamai da masana ilimi ke yi wajen kare ci gaban ƙasa yana daidai da rawar da jami’an tsaro ke takawa, don haka dakatar da gina makarantu ba zai taɓa zama mafita ba. Ya kuma soki shirin ɗaukar ƙarin jami’an tsaro 50,000 yana mai cewa matsalar ba ƙarancin ma’aikata ba ce, illa cin hanci da karkatar da kuɗin samar da tsaro.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, idan an rage cin hanci da almundahanar kuɗin tsaro,  ƴansanda kaɗai za su iya murƙushe ta’addanci da fashi a cikin makonni biyu. Ya yi watsi da batun samar da masu gadin daji, yana cewa rundunonin tsaron ƙasa tuni suna da ƙwarewa da ƙarfin da ya dace wajen daƙile ƴan bindiga idan aka basu ingantaccen shugabanci na gaskiya. Ya tunatar da irin rawar da Sojojin Nijeriya suka taka wajen daidaita ƙasashen Afrika tun daga shekarun 1970, yana mai cewa rashin tsari ne ya sa matsalar cikin gida ta gagari gwamnati.

Baba
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu
  • Abubakar Sulaiman
    ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa
  • Abubakar Sulaiman
    Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata
  • Abubakar Sulaiman
    Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

MASU ALAKA

Baba
Labarai

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano
Labarai

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Next Post
Dalibai 2,199 Sun Amfana Da Tallafin Karatu A Kananan Hukumomin Musawa Da Matazu A Katsina

Dalibai 2,199 Sun Amfana Da Tallafin Karatu A Kananan Hukumomin Musawa Da Matazu A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026
Baba

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

July 27, 2026
Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Baba

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.