Ƙungiyar Limamai da a Jihar Ogun, ta yi watsi da shirin Gwamna Dapo Abiodun, na mayar da makarantun gwamnati ga ƙungiyoyin ƴan mishan, inda ta bayyana matakin a matsayin “abu maras kyawu da tsokana da kuma rashin gaskiya.”
Daily trust ta ruwaito cewa, a makon da ya gabata ne, Abiodun ya bayyana shirin gwamnatinsa na mayar da makarantun mishan a jihar ga iyayensu na asali a wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa haɗin gwiwa a ɓangaren ilimi.
Gwamnan ya bayyana hakan ne, a ranar Juma’a a lokacin da yake karɓar baƙuncin limamin coci a Nijeriya, Archbishop Michael Francis Crotty, a wata ziyarar ban girma da ya kai ofishinsa da ke Oke-Mosan, Abeokuta.
Wakilin ya samu rakiyar Bishop ɗin Katolika na Ijebu-Ode, Francis Obafemi Adesina, Bishop na Abeokuta, Peter Odetoyinbo da sauran jami’an cocin.
“Za mu mayar da dukkan makarantun mishan ga masu su. Muna buƙatar mu haɗa hannu da mutane masu zaman kansu, sannan kuma mu ƙarfafa haɗin gwiwa tare da Coci, domin faɗaɗa ci gaba,” in ji gwamnan.
A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ranar Litinin, Imam Tajudeen Mustafa Adewunmi, babban sakataren ƙungiyar limamai da Alfas ta Jihar Ogun, ƙungiyar ta yi watsi da shirin, inda ta bayyana shi a matsayin wanda ya saɓa wa ƙa’idojin daidaito.
“Wannan manufar, ba kawai babban kuskure ba ne a tarihin ilimin jihar, har ma da cin zarafi tare da haɗari ga ƙa’idodin daidaito, adalci da daidaiton addini a cikin jama’a,” in ji ƙungiyar.
A cewar Limaman, makarantun gwamnati a Jihar Ogun, na kowa da kowa ne, “don haka, akwai buƙatar kawar da irin salon mulkin da da gwamnati ke son dawo da shi yanzu.”
Adewunmi ya gabatar da cewa, “Bari a bayyana wannan tsari ba tare da wata shubuha ba: Wannan matakin na nuna wariya ne gaba-ɗaya, wanda ba za a amince da ita ba kwata-kwata, domin hakan yana nuna a shirye gwamnati take wajen fifita muradun wata ƙungiya ta addini a kan wata.
“Al’ummar Musulmi, waɗanda suka kasance yanki mai ɗimbin yawa da tarihi na Jihar Ogun, ba za su tsaya a yayin da ake shirin yin watsi da ƴancinsu da hankalinsu da kuma gudummawar da suke bayarwa ba, ba za mu yarda da duk wata manufa da take neman a mayar da cibiyoyin gwamnatin da aka gina aka kuma inganta su zuwa ga tsarin ɓangaranci a ƙarƙashin kowace irin fuska ba.”














Discussion about this post