ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’umma Sun Ƙi Amincewa Da Shirin Gwamnatin Ogun Na Mayar Da Makarantu Ga Ƴan Misham

by Sani Anwar
3 months ago

Ƙungiyar Limamai da a Jihar Ogun, ta yi watsi da shirin Gwamna Dapo Abiodun, na mayar da makarantun gwamnati ga ƙungiyoyin ƴan mishan, inda ta bayyana matakin a matsayin “abu maras kyawu da tsokana da kuma rashin gaskiya.”

Daily trust ta ruwaito cewa, a makon da ya gabata ne, Abiodun ya bayyana shirin gwamnatinsa na mayar da makarantun mishan a jihar ga iyayensu na asali a wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa haɗin gwiwa a ɓangaren ilimi.

Gwamnan ya bayyana hakan ne, a ranar Juma’a a lokacin da yake karɓar baƙuncin limamin coci a Nijeriya, Archbishop Michael Francis Crotty, a wata ziyarar ban girma da ya kai ofishinsa da ke Oke-Mosan, Abeokuta.

ADVERTISEMENT

Wakilin ya samu rakiyar Bishop ɗin Katolika na Ijebu-Ode, Francis Obafemi Adesina, Bishop na Abeokuta, Peter Odetoyinbo da sauran jami’an cocin.

“Za mu mayar da dukkan makarantun mishan ga masu su. Muna buƙatar mu haɗa hannu da mutane masu zaman kansu, sannan kuma mu ƙarfafa haɗin gwiwa tare da Coci, domin faɗaɗa ci gaba,” in ji gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ranar Litinin, Imam Tajudeen Mustafa Adewunmi, babban sakataren ƙungiyar limamai da Alfas ta Jihar Ogun, ƙungiyar ta yi watsi da shirin, inda ta bayyana shi a matsayin wanda ya saɓa wa ƙa’idojin daidaito.

“Wannan manufar, ba kawai babban kuskure ba ne a tarihin ilimin jihar, har ma da cin zarafi tare da haɗari ga ƙa’idodin daidaito, adalci da daidaiton addini a cikin jama’a,” in ji ƙungiyar.

A cewar Limaman, makarantun gwamnati a Jihar Ogun, na kowa da kowa ne, “don haka, akwai buƙatar kawar da irin salon mulkin da da gwamnati ke son dawo da shi yanzu.”

Adewunmi ya gabatar da cewa, “Bari a bayyana wannan tsari ba tare da wata shubuha ba: Wannan matakin na nuna wariya ne gaba-ɗaya, wanda ba za a amince da ita ba kwata-kwata, domin hakan yana nuna a shirye gwamnati take wajen fifita muradun wata ƙungiya ta addini a kan wata.

“Al’ummar Musulmi, waɗanda suka kasance yanki mai ɗimbin yawa da tarihi na Jihar Ogun, ba za su tsaya a yayin da ake shirin yin watsi da ƴancinsu da hankalinsu da kuma gudummawar da suke bayarwa ba, ba za mu yarda da duk wata manufa da take neman a mayar da cibiyoyin gwamnatin da aka gina aka kuma inganta su zuwa ga tsarin ɓangaranci a ƙarƙashin kowace irin fuska ba.”

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

MASU ALAKA

Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi
Manyan Labarai

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

July 1, 2026
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Siyasa

Tinubu Ya Shimfiɗa Wa Arewacin Nijeriya Ayyuka Sama Da Kowane Shugaban Ƙasa – Uba Sani

July 1, 2026
Next Post
Akwai Yiwuwar Sake Tsare Ni Dindindin – El-Rufa’i

Akwai Yiwuwar Sake Tsare Ni Dindindin - El-Rufa'i

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.