ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’umma Sun Ƙi Amincewa Da Shirin Gwamnatin Ogun Na Mayar Da Makarantu Ga Ƴan Misham

by Sani Anwar
2 months ago

Ƙungiyar Limamai da a Jihar Ogun, ta yi watsi da shirin Gwamna Dapo Abiodun, na mayar da makarantun gwamnati ga ƙungiyoyin ƴan mishan, inda ta bayyana matakin a matsayin “abu maras kyawu da tsokana da kuma rashin gaskiya.”

Daily trust ta ruwaito cewa, a makon da ya gabata ne, Abiodun ya bayyana shirin gwamnatinsa na mayar da makarantun mishan a jihar ga iyayensu na asali a wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa haɗin gwiwa a ɓangaren ilimi.

Gwamnan ya bayyana hakan ne, a ranar Juma’a a lokacin da yake karɓar baƙuncin limamin coci a Nijeriya, Archbishop Michael Francis Crotty, a wata ziyarar ban girma da ya kai ofishinsa da ke Oke-Mosan, Abeokuta.

ADVERTISEMENT

Wakilin ya samu rakiyar Bishop ɗin Katolika na Ijebu-Ode, Francis Obafemi Adesina, Bishop na Abeokuta, Peter Odetoyinbo da sauran jami’an cocin.

“Za mu mayar da dukkan makarantun mishan ga masu su. Muna buƙatar mu haɗa hannu da mutane masu zaman kansu, sannan kuma mu ƙarfafa haɗin gwiwa tare da Coci, domin faɗaɗa ci gaba,” in ji gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ranar Litinin, Imam Tajudeen Mustafa Adewunmi, babban sakataren ƙungiyar limamai da Alfas ta Jihar Ogun, ƙungiyar ta yi watsi da shirin, inda ta bayyana shi a matsayin wanda ya saɓa wa ƙa’idojin daidaito.

“Wannan manufar, ba kawai babban kuskure ba ne a tarihin ilimin jihar, har ma da cin zarafi tare da haɗari ga ƙa’idodin daidaito, adalci da daidaiton addini a cikin jama’a,” in ji ƙungiyar.

A cewar Limaman, makarantun gwamnati a Jihar Ogun, na kowa da kowa ne, “don haka, akwai buƙatar kawar da irin salon mulkin da da gwamnati ke son dawo da shi yanzu.”

Adewunmi ya gabatar da cewa, “Bari a bayyana wannan tsari ba tare da wata shubuha ba: Wannan matakin na nuna wariya ne gaba-ɗaya, wanda ba za a amince da ita ba kwata-kwata, domin hakan yana nuna a shirye gwamnati take wajen fifita muradun wata ƙungiya ta addini a kan wata.

“Al’ummar Musulmi, waɗanda suka kasance yanki mai ɗimbin yawa da tarihi na Jihar Ogun, ba za su tsaya a yayin da ake shirin yin watsi da ƴancinsu da hankalinsu da kuma gudummawar da suke bayarwa ba, ba za mu yarda da duk wata manufa da take neman a mayar da cibiyoyin gwamnatin da aka gina aka kuma inganta su zuwa ga tsarin ɓangaranci a ƙarƙashin kowace irin fuska ba.”

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Akwai Yiwuwar Sake Tsare Ni Dindindin – El-Rufa’i

Akwai Yiwuwar Sake Tsare Ni Dindindin - El-Rufa'i

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.