ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’umma Sun Ƙi Amincewa Da Shirin Gwamnatin Ogun Na Mayar Da Makarantu Ga Ƴan Misham

by Sani Anwar
3 months ago

Ƙungiyar Limamai da a Jihar Ogun, ta yi watsi da shirin Gwamna Dapo Abiodun, na mayar da makarantun gwamnati ga ƙungiyoyin ƴan mishan, inda ta bayyana matakin a matsayin “abu maras kyawu da tsokana da kuma rashin gaskiya.”

Daily trust ta ruwaito cewa, a makon da ya gabata ne, Abiodun ya bayyana shirin gwamnatinsa na mayar da makarantun mishan a jihar ga iyayensu na asali a wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa haɗin gwiwa a ɓangaren ilimi.

Gwamnan ya bayyana hakan ne, a ranar Juma’a a lokacin da yake karɓar baƙuncin limamin coci a Nijeriya, Archbishop Michael Francis Crotty, a wata ziyarar ban girma da ya kai ofishinsa da ke Oke-Mosan, Abeokuta.

ADVERTISEMENT

Wakilin ya samu rakiyar Bishop ɗin Katolika na Ijebu-Ode, Francis Obafemi Adesina, Bishop na Abeokuta, Peter Odetoyinbo da sauran jami’an cocin.

“Za mu mayar da dukkan makarantun mishan ga masu su. Muna buƙatar mu haɗa hannu da mutane masu zaman kansu, sannan kuma mu ƙarfafa haɗin gwiwa tare da Coci, domin faɗaɗa ci gaba,” in ji gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ranar Litinin, Imam Tajudeen Mustafa Adewunmi, babban sakataren ƙungiyar limamai da Alfas ta Jihar Ogun, ƙungiyar ta yi watsi da shirin, inda ta bayyana shi a matsayin wanda ya saɓa wa ƙa’idojin daidaito.

“Wannan manufar, ba kawai babban kuskure ba ne a tarihin ilimin jihar, har ma da cin zarafi tare da haɗari ga ƙa’idodin daidaito, adalci da daidaiton addini a cikin jama’a,” in ji ƙungiyar.

A cewar Limaman, makarantun gwamnati a Jihar Ogun, na kowa da kowa ne, “don haka, akwai buƙatar kawar da irin salon mulkin da da gwamnati ke son dawo da shi yanzu.”

Adewunmi ya gabatar da cewa, “Bari a bayyana wannan tsari ba tare da wata shubuha ba: Wannan matakin na nuna wariya ne gaba-ɗaya, wanda ba za a amince da ita ba kwata-kwata, domin hakan yana nuna a shirye gwamnati take wajen fifita muradun wata ƙungiya ta addini a kan wata.

“Al’ummar Musulmi, waɗanda suka kasance yanki mai ɗimbin yawa da tarihi na Jihar Ogun, ba za su tsaya a yayin da ake shirin yin watsi da ƴancinsu da hankalinsu da kuma gudummawar da suke bayarwa ba, ba za mu yarda da duk wata manufa da take neman a mayar da cibiyoyin gwamnatin da aka gina aka kuma inganta su zuwa ga tsarin ɓangaranci a ƙarƙashin kowace irin fuska ba.”

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Akwai Yiwuwar Sake Tsare Ni Dindindin – El-Rufa’i

Akwai Yiwuwar Sake Tsare Ni Dindindin - El-Rufa'i

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026
Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

July 25, 2026
Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

July 25, 2026
Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

July 25, 2026
Kalolin Kitso Na Zamani: Yadda Ake Yin Fulani Style

Muhimmancin Kula Da Gashi Domin Lafiyarsa Da Kyawunsa

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.