Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa akwai wani shiri da ake yi domin ɓata masa suna, da hana bayar da shi beli a Babbar Kotun Jihar Kaduna, da kuma jefa shi cikin waɗanda suka aikata manyan laifuffuka.
Ya ce ana ƙoƙarin amfani da rahotannin jaridu marasa tushe domin tabbatar da tsare shi na dindindin, yana mai jaddada cewa shi bai da wata alaƙa da abubuwan da aka ambata.
A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Muyiwa Adekeye, ya fitar a ranar Lahadi, El-Rufai ya ce an fara nuna alamun wannan shiri tun lokacin da aka yi yunƙurin kama shi a filin jirgin Abuja bayan dawowarsa daga Cairo a ranar 12 ga Fabrairu, 2026. Ya ce daga baya ya amsa gayyatar EFCC, inda aka tsare shi kafin a mika shi ga ICPC, kuma har yanzu yana tsare yayin da aka gurfanar da shi a kotuna biyu daban-daban.
- Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
- Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
- Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
- Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
- Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
Sanarwar ta kuma yi nuni da wani rahoto da wata jarida ta wallafa a ranar 18 ga Afrilu, 2026, inda aka ce wasu ‘yan bindiga sun kai hari gidan wani shaida a shari’ar da ake yi da El-Rufai. Ya ce rahoton ya yi ƙoƙarin alaƙanta lamarin da shi, wanda ya kira da shirin ɓata masa suna da hana masa ‘yanci, musamman yayin da ake jiran hukunci kan neman belinsa.
El-Rufai ya jaddada cewa ya umarci lauyoyinsa su ɗauki matakin shari’a kan jaridar bisa ɓata suna, yana mai cewa dole ne a mutunta doka da ‘yancin ɗan ƙasa. Ya kuma bukaci a daina amfani da tsarin shari’a a matsayin makamin danniya, yana mai cewa ya kamata a ba shi cikakken ‘yancin da doka ta tanada yayin da yake fuskantar tuhume-tuhume da ya sha musantawa.














