Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa akwai wani shiri da ake yi domin ɓata masa suna, da hana bayar da shi beli a Babbar Kotun Jihar Kaduna, da kuma jefa shi cikin waɗanda suka aikata manyan laifuffuka.
Ya ce ana ƙoƙarin amfani da rahotannin jaridu marasa tushe domin tabbatar da tsare shi na dindindin, yana mai jaddada cewa shi bai da wata alaƙa da abubuwan da aka ambata.
A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Muyiwa Adekeye, ya fitar a ranar Lahadi, El-Rufai ya ce an fara nuna alamun wannan shiri tun lokacin da aka yi yunƙurin kama shi a filin jirgin Abuja bayan dawowarsa daga Cairo a ranar 12 ga Fabrairu, 2026. Ya ce daga baya ya amsa gayyatar EFCC, inda aka tsare shi kafin a mika shi ga ICPC, kuma har yanzu yana tsare yayin da aka gurfanar da shi a kotuna biyu daban-daban.
- Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin: Za a Gudanar Da Bukukuwa Fiye Da 100 Na “Fitar Da Kayayyaki Zuwa Kasar Sin” a Shekara Ta 2026
- Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki A DPRK
- Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
- ‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
- Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
Sanarwar ta kuma yi nuni da wani rahoto da wata jarida ta wallafa a ranar 18 ga Afrilu, 2026, inda aka ce wasu ‘yan bindiga sun kai hari gidan wani shaida a shari’ar da ake yi da El-Rufai. Ya ce rahoton ya yi ƙoƙarin alaƙanta lamarin da shi, wanda ya kira da shirin ɓata masa suna da hana masa ‘yanci, musamman yayin da ake jiran hukunci kan neman belinsa.
El-Rufai ya jaddada cewa ya umarci lauyoyinsa su ɗauki matakin shari’a kan jaridar bisa ɓata suna, yana mai cewa dole ne a mutunta doka da ‘yancin ɗan ƙasa. Ya kuma bukaci a daina amfani da tsarin shari’a a matsayin makamin danniya, yana mai cewa ya kamata a ba shi cikakken ‘yancin da doka ta tanada yayin da yake fuskantar tuhume-tuhume da ya sha musantawa.















Discussion about this post