An sake samun fargabar afkuwar mummunar ambaliyar ruwa a Nijeriya, bayan wani sabon hasashen da Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya ta fitar, wanda ya sanya al’ummomi 944 a jihohi 21 cikin halin taka-tsantsan game da barazanar ambaliyar ruwa, a tsakanin ranar 2 ga Agusta da 15 ga Agustan 2026.
Ma’aikatar ta bayyana cewa, ɗaruruwan wasu al’ummomin ma na fuskantar barazanar ambaliyar ruwa a matakai daban-daban.
Gwamnati ta yi gargaɗin cewa, al’ummomin da abin ya shafa, na iya fuskantar mummunar ambaliyar ruwa, sakamakon haɗuwar abubuwa da suka haɗa da ci gaba da yin ruwan sama, ƙaruwar ruwan koguna, cikar ƙasa da ruwa, saurin kwararar ruwa a saman ƙasa da kuma cunkoson hanyoyin magudanan ruwa; tare da yin kira ga mazauna yankunan da ke cikin haɗari da su fara ɗaukar matakan kariya nan take.
Dangane da sabon hasashen ambaliyar ruwa da Cibiyar Kula da Gargaɗin Farko kan Ambaliyar Ruwa ta Ƙasa (ƙarƙashin Sashen Kula da Zaizayar Ƙasa, Ambaliyar Ruwa da Yankunan Teku na Ma’aikatar) ta fitar, an sanya ƙarin al’ummomi 406 a jihohi bakwai, cikin rukunin yankunan da ke fuskantar babban haɗari, yayin da al’ummomi 650 a jihohi 13 ke cikin rukunin da ke buƙatar sa ido kan yiwuwar ambaliya ta matsakaicin mataki.
Wannan ya sa jimillar wuraren da ke cikin jerin sa ido kan ambaliyar ruwa na ƙasa ya kai kimanin al’ummomi 2,000 a dukkan jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya (FCT).
Rahoton ya bayyana Jihohin Benuwe, Kogi, Kwara, Neja, Ribas, Edo, Delta, Kuros Riba, Bayelsa, Akwa Ibom, Abiya, Anambira, Ebonyi, Enugu, Imo, Ekiti, Legas, Ogun, Ondo, Osun da Oyo a matsayin yankunan da ke fuskantar barazanar ambaliyar ruwa mafi tsanani a jihohin da hasashen ya shafa.
Daga cikin manyan biranen da al’ummomin da aka sanya a rukunin da ke fuskantar babban haɗarin, akwai Makurdi, Katsina Ala, Gboko da Otukpo a Jihar Benuwe; Lokoja da Idah a Kogi; Fatakwal, Bonny, Okrika da Ahoada a Ribas; Benin City a Edo; Asaba da Warri a Delta; Kalaba a Kuros Riba; Yenagoa a Bayelsa; Uyo, Eket da Oron a Akwa Ibom; Aba da Umuahia a Abiya; Onitsha, Awka da Nnewi a Anambira; Abakaliki a Ebonyi; birnin Inugu; Owerri a Imo; Ado-Ekiti; Legas Island, Lekki, Ikorodu, Apapa, Eti-Osa, Ikeja da Badagry a Lagos; Abeokuta, Ifo da Shagamu a Ogun; Akure da Okitipupa a Ondo; Osogbo da Ile-Ife a Osun; da kuma Ibadan a ihar Oyo.
Ma’aikatar ta bayyana cewa, al’ummomin da aka rarraba a matsayin wuraren da ke da haɗari, suna buƙatar sa ido kan ambaliyar ruwa nan take, shirye-shiryen gaggawa da matakan kariya, yayin da waɗanda ke cikin rukunin masu haɗari ya kamata su ƙara himma wajen sa ido da shirye-shiryen gaggawa, don mayar da martani.
An shawarci al’ummomin da ke wurin da ke da haɗari, da su ci gaba da sa ido a-kai-a-kai, su kuma kula da kayayyakin magudanan ruwa da kuma ƙarfafa wayar da kan jama’a.














