ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kebbi Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Kaimi Wajen Fatattakar Ƴan Bindiga

by Umar Faruk Birnin Kebbi
1 month ago

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya yaba wa Babban Hafsan Sojin Nijeriya bisa tura ƙarin sojoji zuwa Karamar Hukumar Yauri domin ƙarfafa yaƙi da ’yan bindiga. Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin ziyarar duba sabbin sojojin da aka tura yankin, inda ya ce matakin ya zo a daidai lokacin da ake buƙatarsa.

Gwamna Idris ya ce ƙarin sojojin zai taimaka wajen ƙarfafa ayyukan tsaro da dawo da zaman lafiya a Yauri, da Shanga, da Ngaski da sauran yankunan da ke maƙwabtaka da su. Ya bayyana yankin Yauri a matsayin ɗaya daga cikin wuraren da ke fuskantar matsalar tsaro saboda kusancinsa da jihohin Neja da Zamfara, yayin da Fakai ke da iyaka da Sakkwato, kuma Kebbi ke da iyaka da Jamhuriyar Benin.

Ya yaba wa jami’an tsaron da ke aiki a yankin bisa jajircewa da sadaukarwa, tare da tabbatar musu da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da ba su dukkan goyon bayan da suke buƙata. Ya ce tsaro nauyi ne da ya rataya a kan kowa, yana mai jaddada muhimmancin haɗin gwuiwa tsakanin gwamnatin tarayya da ta jiha wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya kuma buƙaci sojojin da su ƙara kaimi wajen fatattakar ’yan bindiga da sauran masu aikata laifuka. Ya ce yana da yaƙinin cewa ƙarin sojojin, tare da horo da ƙwarewar jami’an tsaron Nijeriya, za su taimaka wajen kawo ƙarshen hare-haren da ake kai wa al’ummomin yankin.

Ya ƙara da cewa ya kamata sojojin su ci gaba da bin ’yan bindigar ba tare da gajiyawa ba, domin dawo da cikakken zaman lafiya da bai wa manoman da suka gudu damar komawa gonakinsu. Gwamna Idris ya kuma gode wa jami’an tsaro bisa hidima da sadaukarwarsu, tare da yi musu addu’ar samun nasara da kariya a yayin gudanar da ayyukansu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Umar Faruk Birnin Kebbi
+ postsBio
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi/
    Ƙungiyar Ƙwadago A Kebbi Ta Nemi Mafi Ƙarancin Albashin Na ₦500,000
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi/
    Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi/
    Kungiyar Malaman Jami’ar AFUSTA Za Ta Tsunduma Yajin Aiki
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi/
    An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post

Yadda Birnin Kano Ya Zama Na 9 A Jerin Mafi Yawan Jama’a A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.