Ministan harkokin cikin gida na Benin, Alassane Seidou, a ranar Lahadi ya ce Sojoji sun dakile yunkurin juyin mulkin da wasu gungun sojoji suka yi wanda suka ce, sun soke gwamnatin Shugaba Patrice Talon.
“Wani ƙaramin rukuni ne na sojoji ya fara bore da nufin wargaza tsarin kasar da cibiyoyinta.
- Jihar Kaduna Ta Ƙulla Yarjejeniyar Dala Miliyan 200 Da Ƙasar Sin Don Bunƙasa Noman Zamani
- Babban Magatakardan SCO: Taiwan Yanki Ne Na Kasar Sin Da Ba Za A Iya Balle Shi Ba
“A wannan yanayi, Sojojin Benin da shugabanninsu sun dakile yunkurin,” in ji Seidou.
A safiyar Lahadi, sojoji da suka kira kansu “Kwamitin Soja don mayar da kasa kan turbarta (CMR)”, sun bayyana a talabijin na gwamnati cewa, sun yanke shawarar “cire Mr. Patrice Talon daga mukaminsa na shugaban jamhuriyar”.
A talabijin, sojoji takwas dauke da muggan bindigogi, sanye da kakin soji iri daban-daban, sun kira kansu “Kwamitin Soja wanda zai mayar da ƙasar kan turbarta, kuma ya naɗa wani Laftanar Kanar a matsayin shugaba.














