Mohamed Salah ya bayyana cewa yana jin tamkar Liverpool ta yi watsi da shi, lamarin da ya haifar da saɓani tsakaninsa da kocin ƙungiyar, Arne Slot. Bayan ya fara wasanni uku a jere daga benci, har da wasan da suka tashi 3-3 da Leeds United, ɗan wasan ya ce ba ya fahimtar abin da ya jawo sauyin da aka samu a tsakaninsu. Ya jaddada cewa ya daɗe yana da kyakkyawar mu’amala da Kocin, amma komai ya fara sauyawa cikin gaggawa.
A wata hira da ya yi da manema labarai bayan wasan, Salah ya ce yana jin akwai wani da ke ƙoƙarin ɗora masa laifi kan matsalolin da ƙungiyar ta samu. Ya ce wannan ya sa yake ganin kamar an an ci moriyar ganga, duk da irin gudummawar da ya bayar tsawon shekaru. A cewarsa, bai kamata a sanya shi cikin wannan yanayi ba, musamman ganin irin abubuwan da ya riga ya cimma a ƙungiyar.
- Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?
- Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika
Salah ya ƙara da cewa duk da wannan al’amari, zai ci gaba da goyon bayan Liverpool saboda kulob ɗin ya zama wani ɓangare na rayuwarsa da ta iyalinsa. Ya ce bai taɓa ganin kansa a matsayin wanda ya fi kowa matsayi ba, amma ya kamata a san matsayin da ya kai a ƙungiyar. Ya bayyana cewa irin wannan rashin adalcin ba shi ne ya dace da shi ko da wani ɗan wasa ba.
Duk da kwantiragin shekaru biyu da ya sanya hannu a watan Afrilu, Salah ya ce yanzu ba shi da tabbas game da makomarsa a Liverpool. Ɗan wasan zai baro ƙungiyar a ranar 15 ga Disamba domin halartar gasar cin kofin Afrika, yana mai cewa komai zai iya faruwa bayan gasar.














