Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya Kai ziyara birnin Beijing domin kulla yarjejeniyoyi da Gwamnatin kasar Sin da Jihar Kaduna kan shirin aikin Norman Kaji Wanda ake sa ran zai samar da ayyuka kai tsaye da na wucin-gadi har 350,000, tare da samar da sama da dala miliyan 450 a shekara.
A Wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar Kaduna Malam Ahmed Maiyaki ya fitar ya bayyana cewa: “Ziyarar ta biyo bayan tattaunawa mai zurfi da aka yi a Nijeriya da Jakadan kasar Sin a Nijeriya Ambassador Yu Dunhai.”
Gwamna Sani yana tare da tawagar Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Darakta-Janar na bun kasa Kasuwacin Nijeriya da kasar Sin , Mista Joseph Tegba, lamarin da ke nuna muhimmancin aikin a matakin ƙasa baki ɗaya.
“Aikin, wanda kudinsa ya kai dala 200 miliyan, na da nufin ƙarfafa tsaron abinci, hanzarta masana’antar harkar noma, ƙara fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje, tare da mayar da Kaduna jagora a harkar noman Zamani “ in ji sanarwar.
Malam Ahmed Maiyaki, ya ce: “Zuwar Gwamna Uba Sani Beijing na nuna jajircewar Jihar Kaduna wajen kafa haɗin gwiwa masu tasiri waɗanda ke kawo ci gaban tattalin arziki mai ɗorewa. Wannan muhimmin aikin kiwon kaji zai samar da dubban ayyuka, ƙarfafa tsaron abinci, tare da mayar da Kaduna jagora a nahiyar Afrika a bangaren agribusiness na zamani.”
Gwamnatin Jihar Kaduna, ƙarƙashin shugabancin Gwamna Sani, na ci gaba da jajircewa wajen jawo manyan jarin duniya domin samar da ci gaban tattalin arziki mai faɗaɗa damar ayyuka ga matasa.
“Gwamna Uba Sani ya kuma bayyana godiyarsa ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, bisa zaɓar Kaduna a matsayin jihar gwaji ta wannan muhimmin shiri, da kuma ga Gwamnatin Jamhuriyar Jama’ar China bisa ci gaba da haɗin gwiwa,” in ji sanarwar.














