ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago

Rundunar ‘yansandan Jihar Kogi ta fara bincike kan mutuwar wata malamar makarantar firamare da ake zargin an yi wa duka saboda ta ladabtar da wani ɗalibi a ƙaramar hukumar Olamaboro ta jihar.

Rundunar ta bayyana cewa an shigar da ƙarar a shalƙwatar ‘yansanda ta Olamaboro ranar 25 ga Yuni, 2026, kuma ana bincikenta a matsayin laifin kisan kai.

Jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar, SP Oyiza Salisu Afusat, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

Binciken farko ya nuna cewa a ranar 18 ga Yuni, wani mutum mai suna Abdullahi Ishaka tare da wasu mata biyu sun je makarantar Brains Minds Nursery and Primary School da ke Ugbamaka, inda ake zargin sun kai wa wata malama mai suna Maryam Usman hari saboda ta ladabtar da wani ɗalibi.

Maryam Usman mai shekara 30 ta samu munanan raunuka sakamakon harin. An fara ba ta magani a wani asibiti da ke Ugbamaka kafin daga bisani a tura ta zuwa asibitin Iko-Ojo da ke Okpo domin ci gaba da jinya.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

Sai dai malamar ta rasu a ranar 25 ga Yuni sakamakon raunukan da ta samu. Afusat ta ce jami’an ‘yansanda sun kai ziyara wurin da lamarin ya faru da kuma gidan marigayiyar bayan an kai rahoton, inda suka gudanar da binciken farko tare da tattara bayanai.

Ta ƙara da cewa ana shirye-shiryen kai gawar marigayiyar zuwa Babban Asibitin Ankpa domin a yi binciken gawar da tantance musabbabin mutuwarta.

Rundunar ta ce waɗanda ake zargi sun tsere kafin isowar jami’an ‘yansanda, amma ana ci gaba da ƙoƙarin kamo su. Ta bayyana cewa da zarar an kama su, za a miƙa shari’ar ga sashin Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) domin ci gaba da cikakken bincike.

Rundunar ‘yansandan Jihar Kogi ta jaddada aniyarta ta tabbatar da cewa an hukunta duk waɗanda ke da hannu a wannan lamari bisa doka.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano
  • Abubakar Sulaiman
    Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure
  • Abubakar Sulaiman
    Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah
  • Abubakar Sulaiman
    Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

MASU ALAKA

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
Ra'ayi Riga

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027
Labarai

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

July 19, 2026
Next Post
Atiku Ya Yi Zargin Ana Shirin Hana ADC Shiga Zaɓen 2027

Atiku Ya Yi Zargin Ana Shirin Hana ADC Shiga Zaɓen 2027

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026
Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

July 19, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

July 19, 2026
Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

July 19, 2026
An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.