ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

by Abubakar Sulaiman
1 hour ago

Rundunar ‘yansandan Jihar Kogi ta fara bincike kan mutuwar wata malamar makarantar firamare da ake zargin an yi wa duka saboda ta ladabtar da wani ɗalibi a ƙaramar hukumar Olamaboro ta jihar.

Rundunar ta bayyana cewa an shigar da ƙarar a shalƙwatar ‘yansanda ta Olamaboro ranar 25 ga Yuni, 2026, kuma ana bincikenta a matsayin laifin kisan kai.

Jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar, SP Oyiza Salisu Afusat, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

Binciken farko ya nuna cewa a ranar 18 ga Yuni, wani mutum mai suna Abdullahi Ishaka tare da wasu mata biyu sun je makarantar Brains Minds Nursery and Primary School da ke Ugbamaka, inda ake zargin sun kai wa wata malama mai suna Maryam Usman hari saboda ta ladabtar da wani ɗalibi.

Maryam Usman mai shekara 30 ta samu munanan raunuka sakamakon harin. An fara ba ta magani a wani asibiti da ke Ugbamaka kafin daga bisani a tura ta zuwa asibitin Iko-Ojo da ke Okpo domin ci gaba da jinya.

LABARAI MASU NASABA

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Sai dai malamar ta rasu a ranar 25 ga Yuni sakamakon raunukan da ta samu. Afusat ta ce jami’an ‘yansanda sun kai ziyara wurin da lamarin ya faru da kuma gidan marigayiyar bayan an kai rahoton, inda suka gudanar da binciken farko tare da tattara bayanai.

Ta ƙara da cewa ana shirye-shiryen kai gawar marigayiyar zuwa Babban Asibitin Ankpa domin a yi binciken gawar da tantance musabbabin mutuwarta.

Rundunar ta ce waɗanda ake zargi sun tsere kafin isowar jami’an ‘yansanda, amma ana ci gaba da ƙoƙarin kamo su. Ta bayyana cewa da zarar an kama su, za a miƙa shari’ar ga sashin Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) domin ci gaba da cikakken bincike.

Rundunar ‘yansandan Jihar Kogi ta jaddada aniyarta ta tabbatar da cewa an hukunta duk waɗanda ke da hannu a wannan lamari bisa doka.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina
  • Abubakar Sulaiman
    Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha
  • Abubakar Sulaiman
    An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

MASU ALAKA

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina
Labarai

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

June 29, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha
Manyan Labarai

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja
Manyan Labarai

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

June 29, 2026
Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

June 29, 2026
Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

June 28, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.