Rundunar ‘yansandan Jihar Kogi ta fara bincike kan mutuwar wata malamar makarantar firamare da ake zargin an yi wa duka saboda ta ladabtar da wani ɗalibi a ƙaramar hukumar Olamaboro ta jihar.
Rundunar ta bayyana cewa an shigar da ƙarar a shalƙwatar ‘yansanda ta Olamaboro ranar 25 ga Yuni, 2026, kuma ana bincikenta a matsayin laifin kisan kai.
Jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar, SP Oyiza Salisu Afusat, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi.
Binciken farko ya nuna cewa a ranar 18 ga Yuni, wani mutum mai suna Abdullahi Ishaka tare da wasu mata biyu sun je makarantar Brains Minds Nursery and Primary School da ke Ugbamaka, inda ake zargin sun kai wa wata malama mai suna Maryam Usman hari saboda ta ladabtar da wani ɗalibi.
Maryam Usman mai shekara 30 ta samu munanan raunuka sakamakon harin. An fara ba ta magani a wani asibiti da ke Ugbamaka kafin daga bisani a tura ta zuwa asibitin Iko-Ojo da ke Okpo domin ci gaba da jinya.
Sai dai malamar ta rasu a ranar 25 ga Yuni sakamakon raunukan da ta samu. Afusat ta ce jami’an ‘yansanda sun kai ziyara wurin da lamarin ya faru da kuma gidan marigayiyar bayan an kai rahoton, inda suka gudanar da binciken farko tare da tattara bayanai.
Ta ƙara da cewa ana shirye-shiryen kai gawar marigayiyar zuwa Babban Asibitin Ankpa domin a yi binciken gawar da tantance musabbabin mutuwarta.
Rundunar ta ce waɗanda ake zargi sun tsere kafin isowar jami’an ‘yansanda, amma ana ci gaba da ƙoƙarin kamo su. Ta bayyana cewa da zarar an kama su, za a miƙa shari’ar ga sashin Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) domin ci gaba da cikakken bincike.
Rundunar ‘yansandan Jihar Kogi ta jaddada aniyarta ta tabbatar da cewa an hukunta duk waɗanda ke da hannu a wannan lamari bisa doka.













