Sauƙi ya samu a Tashar Jiragen Ruwa ta Apapa biyo bayan ƙoƙarin da Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Ƙasa NPA ta yi a ƙarƙashin shugabancin Shugaban Hukumar Dakta Abubakar Ɗantsoho ta yi, na rage cunko, musamman na manyan motoci.
Kwamitin da ke kula da shige da fice manyan motoci da sauran kayan da ake shiga da su cikin Tashar ta Apapa da ke a jihar Legos wato LASTCOC ne, yayi wannan jinjinar.
- Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho
- Tsarin ‘Digital Call-Up’ Ta NPA Ya Samu Karɓuwa A Tashar Jiragen Ruwa Na Onne
Kazalika, kwamtin ya ɗora samun wannan gagaruwar nasarar bisa jaoranci na gari, na Shugaban Hukumar Dakta Abubakar Ɗantsho.
A cewar kwamntin, aikin gyara babbar Gadar Marine Bridge da Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya ta gudanar a kwanan baya, hakan ya taimaka matuƙa wajen rage cunkoson da ababen hawa musamman manyan moci ke fuskanta a kan hanyar Ijora–Apapa
Kazalika, kwamnatin na LASTCOC ya bayyana cewa, ba dan jajircewar da Manajan Tashar ta Apapa da tawagarsa ba, da ƙalubalen na cunkoson manyan motocin, ya ƙara munana.
A cewar Shugaban kwamtin na LASTCOC Mista Shittu Lukmon, aikin gyra hanyar ya taimaka ganin cewa, ana shafe sa’oi 24 ba tare da an fuskanci wani cunkoson ababen hawa a hanyar ba.
Shugaban ya ƙara da cewa, hakan ya kuma samar da sauƙin gudanar da fitar da kaya daga cikin Tashar ta Apapa ba tare da wani jinkiri ba.
Ya ci gaba da cewa, bisa ci gaba da gudanar da gyran hanyar, Hukumar ta NPA na ci gaba da yin ƙoƙari wajen ganin manyan motocin na ci gaba da gudanar da zirga-zirgarsu ta shiga da kuma fita daga Tashar ta Apapa.
Lukmon ya danganta Manajan na Apapa a matsayin jajirtacce, wanda ya sanar da cewa, hatta a cikin mako Manajan na fitowa domin sanya ido kan aikin domin ya tabbatar komai na tafiya, bisa ƙa’ida, ba tare da samun cunkoso ba.
“Wannan ƙoƙarin na Manajan abin yabawa ne, domin ban taɓa ganin wani Manaja na NPA da ya kasance jajirtacce kamar shi ba,” A cewar Shugaban kwamtin.














