An kaddamar da wata sabuwar hanyar jigilar manyan kwantenoni zuwa yankunan yammacin Afirka, a tashar jiragen ruwa da ke birnin Qingdao na lardin Shandong na arewacin kasar Sin, hanyar da ta kasance irinta ta biyu da aka kaddamar a bana a tashar, ta jigilar hajoji zuwa nahiyar Afirka.
Wasu rahotanni sun ce, gaba daya jiragen ruwa guda 13 ne ke zirga-zirga ta wannan sabuwar hanya. Kuma sabuwar hanyar jigilar manyan kwantenonin da aka kaddamar a wannan karo, wadda daya ce daga cikin muhimman tashoshin jiragen ruwa da ke arewacin kasar Sin, tana kai wa ga wasu muhimman cibiyoyin kasuwanci da ke yammacin Afirka, ciki har da Tema da Lagos, al’amarin da ya yi matukar takaita yawan lokutan da ake bukata na jigilar hajoji tsakanin yankin kasar Sin da yammacin Afirka.
Kawo yanzu, an riga an kaddamar da wasu hanyoyi 11 na jigilar manyan kwantenoni zuwa nahiyar Afirka, a tashar jiragen ruwa ta Qingdao, hanyoyin da suka shafi muhimman kasuwannin da ke gabashi, da yammaci, gami da arewacin Afirka, tare kuma da hade sassan sufurin ruwa da na jiragen kasa na sassan kasa da kasa, al’amarin da ya taimaka wajen kafa wani ingantaccen tsarin jigilar kayayyaki, na hadin gwiwar jiragen ruwa da na kasa, wanda ya hade sassan kasashe 23, da suke raya shawarar Ziri Daya da Hanya Daya tare da kasar Sin. (Murtala Zhang)















Discussion about this post