Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Mohammed Matawalle, ya ce zai saya wa gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, fom ɗin takarar gwamna a jam’iyyar APC domin sake tsayawa takara a zaɓen 2027. Ya bayyana haka ne yayin wani taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da aka gudanar a Gusau tare da halartar manyan jiga-jigan siyasa na jihar.
A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya ce manufar taron ta wuce siyasa, inda ya bayyana shi a matsayin yunƙuri na haɗin kai domin ceto jihar daga matsaloli, musamman na tsaro. Ya ƙara da cewa sun cimma matsaya na haɗa kai domin tabbatar da ci gaba da kuma aiwatar da muhimman ayyuka a faɗin ƙananan hukumomi 14 na jihar.
Haka kuma, tsofaffin gwamnoni da sauran shugabannin sun jaddada buƙatar zaman lafiya da haɗin kai a cikin APC, suna mai cewa hakan zai taimaka wajen dawo da daidaito da kuma ƙarfafa jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.
A ƙarshe, Matawalle ya buƙaci magoya bayansa su ba Gwamna Lawal cikakken goyon baya, yana mai cewa sun gamsu da yadda yake tafiyar da harkokin mulki da kuma irin ci gaban da ake samu a jihar.















Discussion about this post