Jami’an tsaro sun kama Bello Bodejo, mai neman takarar Sanatan Taraba ta Tsakiya a ƙarƙashin jam’iyyar APC, a daren Alhamis a Jalingo, babban birnin Jihar Taraba.
Bodejo, wanda shi ne shugaban Miyetti Allah Kautal Hore, ya isa Jalingo ne da jirgi mai zaman kansa ta filin jirgin saman Danbaba Suntai Airport da misalin ƙarfe 1:20 na rana, inda dubban magoya bayansa daga ƙananan hukumomin Taraba ta Tsakiya suka tarɓe shi.
Mai taimaka masa, Umar, ya ce an kama Bodejo ne bayan ya kai ziyara wasu ofisoshin jami’an tsaro tare da abokan siyasarsa, jim kaɗan bayan ya yi wa magoya baya jawabi a sakatariyar APC ta jihar. Ya ce an sallami wadanda suka raka shi yayin da aka tsare shi, kuma har yanzu ba su san inda aka kai shi ba.
Rahoton Daily Trust ta bayyana cewa; jami’an tsaron da suka raka Bodejo daga Abuja zuwa Jalingo su ne suka kama shi daga baya, yana mai cewa har yanzu ba a sanar da su dalilin kama shi ba. Kafin kama shi, Bodejo ya bayyana wa manema labarai cewa ya sayi fom ɗin takarar sanata kuma ba zai janye wa kowa ba duk da matsin lamba.
Wannan ba shi ne karo na farko da ake kama Bodejo ba. A shekarar 2024, jami’an DSS sun kama shi bisa zargin kafa ƙungiyar sintiri a Jihar Nasarawa. Har yanzu dai ba a tabbatar ko sabon kamen yana da nasaba da siyasa ko kuma batun tsaro ba.













Discussion about this post