A ci gaba da tsare-tsare na zamanantar da sashen kiwo na Nijeriya, Gwamnatin Jihar Jigawa, ta kulla hadin gwiwar fasaha da ‘Kamfanin L&Z Integrated Dairy and Farms da Sahel Consulting’, domin aiwatar da shirin ci gaba da bunkasa harkokin kiwo a Nijeriya (ALDDNa).
Wannan yunkuri, wanda aka samar don mayar da kiwo zuwa wata sana’ar kasuwanci mai riba da yawa, na neman magance kalubale biyu na karancin noman kiwo da rigingimun manoma da makiyaya ta hanyar samar da canjin yanayin halitta da hada kudi.
Da yake jawabi a wajen kaddamar da aikin tattara madara da kayan aikin kiwon dabbobi a Dutse, Kwamishinan Raya Dabbobi, Farfesa Salem Abdulrahman Lawan, ya koka game da rashin ingancin kiwo na gargajiya.
Lawan ya bayyana cewa, jihar na kammala shirye-shiryen kafa cibiyar samar da maniyyi, domin saukaka manyan hanyoyin noma.
“Idan aka duba tarihi, Indiya ta kasance kamar Nijeriya a fannin noma, amma sai suka kafa kansu. A yau, suna da masu fasaha sama da 300,000 da ke da hannu wajen kawo kyakkyawan sauyi, don haka; mu ma muna so mu kwaikwayi hakan a Jihar Jigawa,” in ji shi.
Aikin ALDDN, wanda Sahel Consulting ke jagoranta, yana mayar da hankali ne, ba kawai kan ilmin halitta ba, har ma a kan tattalin arzikin mata makiyaya.
Shugaban tawagar masu tallafa wa abokan aikin, Abdullahi Baba Muhammed, ya jaddada cewa; rabon kayan aiki, tun daga na’urorin auna zafin jiki na asibiti da safar hannu ta tiyata zuwa gwangwani, bakin karfe, an danganta su da wata manufa mai dorewa.
Ya ce, ya zuwa yanzu, shirin ya samu nasarar kai wa ga gamayyar kungiyoyin hadin guiwa guda 32 a fadin jihar, kuma ta hanyar samar da na’urorin kiwon lafiya na dabbobi da tabbatar da tsaftar muhalli, hadin gwiwar, na nufin samar da wani tsari na tsarin canjin dabbobi na kasa (NLTP).















Discussion about this post