Mataimakin Shugaban kasa Kashim Shettima ya bayyana cewa babu wani zuba jari a bangaren ilimi da za’a daue shi tamkar wata Caca ce aka yi, domin kuwa shi ya tsaya kai da fata cewa bangaren na ilimi yake jagora kan samu gaba ta kasance gwanin ban sha’awa ga Nijeriya da ‘yan Nijeriya.
Bugu da kari ya yi wa ilimi kallon wani babban ginshiki ne na ci gaba, ci gaban tattali arziki da kuma ba kowa dama domin shi/ita a samu tsayawa da kafafu.
- Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Lalata Sansanonin Ƴan Ta’adda A Borno
- DSS Ta Kama Jami’inta Kan Zargin Cin Zarafin Yarinya ‘Yar Shekara 16
Ya yi wannan jawabin ne lokacin da aka yi bukukuwan yaye dalibai na hadin gwiwa na Jami’ar Kashim Ibrahim a Jihar Borno , inda aka yaye jimillar dalibai 2,294 wadanda suka kammala karatunsu a shekarun karau uku wato – 2022/2023, 2023/2024 da kuma 2024/2025, mataimakin Shugaban kasar ya yi kira da wadanda suka kammala karatunsu na Jami’a su dauki kansu a matsayin wani wuri ne daga wurinsu inda za’a koyi tafiyar da gaskiya,rikon amana, son juna, da kuma inganci.
Ya kara jaddada cewa halayen da za su rika nunawa lokacin mu’amalarsu da al’umma ta haka ne, za’a iya gane cewa ashe dukkan wadancan halaye daga can ne kuka kara koyonsu domin makarantu ba karatu kadai suke koyawa ba,da akwai anu’oin tarbiyyar bayan tarniyyar da suka samu daga gida.
“Babu wata harkar zuba jari a ilimi da za ayi a dauke ta cewa matsayinta daya da harkar Caca. Wani tsari ne aka yi domin a gaba a sau dama ta kasancewa a yanayi wanda kowa zai ce gara da aka yi hakan.
Ya kara bayanin cewa ‘’Duk inda lamarin ilimi ya kai mutum ai yana tafiya da sunan ne, don haka za ku rika tafiya ce a sunan Jami’ar Kashim Ibrahim saboda ai can ne aka kara wayar maku da kai kan yadda rayuwa take da kuma yadda ya dace a tafiyar da ita, bayan irin tarbiyar da kuka samu a gida, ba wai ilimin zalla bane da akwai dabi’un da ake koyo daga makaranta. Hakanan ma kada ku bari a yaudare ku har a kai ga jan ra’ayinku har ku kai ga yin abinda zai zubar da mutuncunku, zuri’arku, da kuma makarantar da kuka yi kamar yadda ya bayyana,”.
Shettima ya bayyana cewa Jihar Borno da gwamnatin ta, ta san a bubuwan da za su iya faruwa a gaba sanadiyar yi wa harkar ilimi rikon sakainar kashi, tun da har, aka yi hakuri da shekarun da aka bata saboda lamarin rashin tsaro sanadiyar fadace- fadacen ta’addanci.
“Borno ta san irin yanayin da ta shiga a shekarun da aka bata da yadda suka kasance ba a maganar ilimi sai ta zaman lafiya ake nema.Amma suk da hakan al’ummar suka yi hakuri, al’ummar suka zabi ci gaba jajircewa duk da yake akwai abubuwan da aka rasa masu muhimmanci kamar yadda bayanin nasa ya nuna.
Ya ce wadanda suka kammala karatun jami’a sune wani babban ginshiki ne na ita Jami’armataimakin Shuban kasar ya tunatar da su cewa, Tarihi fa ya maida su suna da wata babbar gudunmawa da za su bada gaba tare da su.
“Ku ne kuka fara kammala karatu a wannan Jami’a.Tarihi zai yi bayani kan wannan Jami’ai ne ta yadda kuka tafiyar da rayuwarku.”
Ya jinjina wa wadanda nauyin koyarwa da Shugabancin Jami’ar ya rataya kansu, har da mutumin da ya fara jagorantar ta a matsayin mataimakin Shugban jami’ari, jagororinta na yanzu, Malamai, ma’aikata, saboda abinda ya kira da sunan “babban ginshikin da suka yi amfani da shi wajen fara lamarin koyarwa a tsakiyar Arewa maso gabas.”















Discussion about this post