ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nemi A Hukunta Likitocin Da Suka Manta Da Almakashi A Cikin Wata Mata Da Ya Yi Sanadiyyar Mutuwarta

by Idris Aliyu Daudawa
5 months ago
Almakashi

Wani dangi a Kano ya zargi Asibitin ‘Abubakar Imam Urology’ da sakaci bayan mutuwar wata matar aure a dangin mai suna Aishatu Umar, wacce ake zargin ta sha fama da matsanancin ciwon ciki na tsawon watanni bayan tiyatar da aka yi mata inda aka bar mata almakashi a cikin cikinta.

Wani ɗan uwanta, Abubakar Mohammed, ya bayyana hakan a wani rubutu da ya yi a shafukan sada zumunta inda ya ɗora hoton marigayiyar da kuma hoton na’urar haske da aka ɗauka wanda ya nuna almakashin da ake zargin an manta da shi a jikin matar bayan tiyatar.

  • Rukunin Ba Da Tallafin Jinya Na Sin Da Asibitin Nijar Sun Gudanar Da Aikin Jinya Kyauta
  • Barin Almakashin Tiyata Acikin Ciki: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Ma’aikatan Asibiti 3 

Mohammed ya ce, Aishatu ta rasu da misalin karfe 1 na dare a ranar Litinin bayan ta sha fama da ciwon da ya daɗe yana damunta tun bayan tiyatar da aka yi mata a asibitin a watan Satumban 2025.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, matar wacce ƴar uwar matarsa ce, ta kamu ne da rashin lafiya a Kano, inda kuma aka kai ta cibiyar kula da cututtukan da suka shafi mafitsara don yi mata tiyata. Ya yi iƙirarin cewa, jim kaɗan bayan tiyatar, Aishatu Umar ta fara jin matsanancin ciwon ciki inda ta riƙa komawa asibitin akai-akai.

“Bayan tiyatar, ta sha fama da matsanancin ciwon ciki. Duk lokacin da ta koma asibitin, maganin rage raɗaɗi kawai suke bata,” in ji Mohammed.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Mohammed ya ƙara da cewa, kwana biyu kacal kafin mutuwarta aka gudanar da gwaje-gwajen lafiya wanda ya kai ga ɗaukar hoton na’urar haske, wanda ya nuna cewa an bar almakashi a cikin jikinta a lokacin tiyatar watan Satumba.

Ya ce, an fara shirye-shiryen yin tiyatar gyara, amma Aishatu ta mutu a ranar Litinin, 12 ga Janairu, 2026, kafin a yi tiyatar.

Bayan zarge-zargen, Hukumar Kula da Asibitoci ta Jihar Kano ta ba da umarnin a gudanar da cikakken bincike kan lamarin. A sanarwar da jami’ar watsa labarai na asibintin, Samira Suleiman ta sanya wa hannu ta bayyana cewa, gwamnatin Jihar Kano ta umarci a gudanar da bincike na musamman a kan lamarin ta kuma dakatar da wasu ma’aikata uku da suka gudanar da aikin nan take ta kuma miƙa ta’aziyya ga iyalai da al’umma a kan rasuwar matar.

Almakashi
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Ƴan Nijeriya Sun Yi Amfani Da Litar Fetur Sama Da Miliyan 63.7 A Iya Watan Disamba

Ƴan Nijeriya Sun Yi Amfani Da Litar Fetur Sama Da Miliyan 63.7 A Iya Watan Disamba

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.