ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nemi A Hukunta Likitocin Da Suka Manta Da Almakashi A Cikin Wata Mata Da Ya Yi Sanadiyyar Mutuwarta

by Idris Aliyu Daudawa
5 months ago
Almakashi

Wani dangi a Kano ya zargi Asibitin ‘Abubakar Imam Urology’ da sakaci bayan mutuwar wata matar aure a dangin mai suna Aishatu Umar, wacce ake zargin ta sha fama da matsanancin ciwon ciki na tsawon watanni bayan tiyatar da aka yi mata inda aka bar mata almakashi a cikin cikinta.

Wani ɗan uwanta, Abubakar Mohammed, ya bayyana hakan a wani rubutu da ya yi a shafukan sada zumunta inda ya ɗora hoton marigayiyar da kuma hoton na’urar haske da aka ɗauka wanda ya nuna almakashin da ake zargin an manta da shi a jikin matar bayan tiyatar.

  • Rukunin Ba Da Tallafin Jinya Na Sin Da Asibitin Nijar Sun Gudanar Da Aikin Jinya Kyauta
  • Barin Almakashin Tiyata Acikin Ciki: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Ma’aikatan Asibiti 3 

Mohammed ya ce, Aishatu ta rasu da misalin karfe 1 na dare a ranar Litinin bayan ta sha fama da ciwon da ya daɗe yana damunta tun bayan tiyatar da aka yi mata a asibitin a watan Satumban 2025.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, matar wacce ƴar uwar matarsa ce, ta kamu ne da rashin lafiya a Kano, inda kuma aka kai ta cibiyar kula da cututtukan da suka shafi mafitsara don yi mata tiyata. Ya yi iƙirarin cewa, jim kaɗan bayan tiyatar, Aishatu Umar ta fara jin matsanancin ciwon ciki inda ta riƙa komawa asibitin akai-akai.

“Bayan tiyatar, ta sha fama da matsanancin ciwon ciki. Duk lokacin da ta koma asibitin, maganin rage raɗaɗi kawai suke bata,” in ji Mohammed.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Mohammed ya ƙara da cewa, kwana biyu kacal kafin mutuwarta aka gudanar da gwaje-gwajen lafiya wanda ya kai ga ɗaukar hoton na’urar haske, wanda ya nuna cewa an bar almakashi a cikin jikinta a lokacin tiyatar watan Satumba.

Ya ce, an fara shirye-shiryen yin tiyatar gyara, amma Aishatu ta mutu a ranar Litinin, 12 ga Janairu, 2026, kafin a yi tiyatar.

Bayan zarge-zargen, Hukumar Kula da Asibitoci ta Jihar Kano ta ba da umarnin a gudanar da cikakken bincike kan lamarin. A sanarwar da jami’ar watsa labarai na asibintin, Samira Suleiman ta sanya wa hannu ta bayyana cewa, gwamnatin Jihar Kano ta umarci a gudanar da bincike na musamman a kan lamarin ta kuma dakatar da wasu ma’aikata uku da suka gudanar da aikin nan take ta kuma miƙa ta’aziyya ga iyalai da al’umma a kan rasuwar matar.

Almakashi
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Ƴan Nijeriya Sun Yi Amfani Da Litar Fetur Sama Da Miliyan 63.7 A Iya Watan Disamba

Ƴan Nijeriya Sun Yi Amfani Da Litar Fetur Sama Da Miliyan 63.7 A Iya Watan Disamba

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.