ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nemi A Hukunta Likitocin Da Suka Manta Da Almakashi A Cikin Wata Mata Da Ya Yi Sanadiyyar Mutuwarta

by Idris Aliyu Daudawa
8 months ago
Almakashi

Wani dangi a Kano ya zargi Asibitin ‘Abubakar Imam Urology’ da sakaci bayan mutuwar wata matar aure a dangin mai suna Aishatu Umar, wacce ake zargin ta sha fama da matsanancin ciwon ciki na tsawon watanni bayan tiyatar da aka yi mata inda aka bar mata almakashi a cikin cikinta.

Wani ɗan uwanta, Abubakar Mohammed, ya bayyana hakan a wani rubutu da ya yi a shafukan sada zumunta inda ya ɗora hoton marigayiyar da kuma hoton na’urar haske da aka ɗauka wanda ya nuna almakashin da ake zargin an manta da shi a jikin matar bayan tiyatar.

  • Rukunin Ba Da Tallafin Jinya Na Sin Da Asibitin Nijar Sun Gudanar Da Aikin Jinya Kyauta
  • Barin Almakashin Tiyata Acikin Ciki: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Ma’aikatan Asibiti 3 

Mohammed ya ce, Aishatu ta rasu da misalin karfe 1 na dare a ranar Litinin bayan ta sha fama da ciwon da ya daɗe yana damunta tun bayan tiyatar da aka yi mata a asibitin a watan Satumban 2025.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, matar wacce ƴar uwar matarsa ce, ta kamu ne da rashin lafiya a Kano, inda kuma aka kai ta cibiyar kula da cututtukan da suka shafi mafitsara don yi mata tiyata. Ya yi iƙirarin cewa, jim kaɗan bayan tiyatar, Aishatu Umar ta fara jin matsanancin ciwon ciki inda ta riƙa komawa asibitin akai-akai.

“Bayan tiyatar, ta sha fama da matsanancin ciwon ciki. Duk lokacin da ta koma asibitin, maganin rage raɗaɗi kawai suke bata,” in ji Mohammed.

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Mohammed ya ƙara da cewa, kwana biyu kacal kafin mutuwarta aka gudanar da gwaje-gwajen lafiya wanda ya kai ga ɗaukar hoton na’urar haske, wanda ya nuna cewa an bar almakashi a cikin jikinta a lokacin tiyatar watan Satumba.

Ya ce, an fara shirye-shiryen yin tiyatar gyara, amma Aishatu ta mutu a ranar Litinin, 12 ga Janairu, 2026, kafin a yi tiyatar.

Bayan zarge-zargen, Hukumar Kula da Asibitoci ta Jihar Kano ta ba da umarnin a gudanar da cikakken bincike kan lamarin. A sanarwar da jami’ar watsa labarai na asibintin, Samira Suleiman ta sanya wa hannu ta bayyana cewa, gwamnatin Jihar Kano ta umarci a gudanar da bincike na musamman a kan lamarin ta kuma dakatar da wasu ma’aikata uku da suka gudanar da aikin nan take ta kuma miƙa ta’aziyya ga iyalai da al’umma a kan rasuwar matar.

Almakashi
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi

MASU ALAKA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
Ƴan Nijeriya Sun Yi Amfani Da Litar Fetur Sama Da Miliyan 63.7 A Iya Watan Disamba

Ƴan Nijeriya Sun Yi Amfani Da Litar Fetur Sama Da Miliyan 63.7 A Iya Watan Disamba

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.