Hukumomin Ƙaramar Hukumar Ungogo da ke Jihar Kano, sun bayar da umarnin rufe makarantar Al-Hadeed Inusawa mai zaman kanta, ba tare da wani ɓata lokaci ba, sakamakon zargin da ake yi wa wani malami kan yin fyaɗe da ake tuhumarsa a gaban kotu.
Kansilan ilimi na ƙaramar hukumar, Malam Abdullahi Wakili ne ya bayar da wannan umarni a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, 18 ga Mayun 2026.
A cewar sanarwar, rufewar ta biyo bayan zargin da ake yi wa wani malami a makarantar na cin zarafin wasu yara mata ƙanana, lamarin da ya sa hukumomin ilimi suka shiga al’amarin cikin gaggawa.
Shugaban ƙaramar hukumar, Hon. Tijjani Amiru Bilyaminu, ya ce; majalisar za ta tabbatar da bin diddigin lamarin da kuma tabbatar da adalci ta hanyar da ta dace.
Ya kuma jaddada ƙudirin majalisar na tabbatar da kare yara da kuma tsaurara matakan tsaro a duk makarantun yankin, domin daƙile afkuwar irin wannan lamari.
Wanda ake zargin, mai suna Uncle Kamal, an gurfanar da shi a gaban wata kotun majistare da ke unguwar No-man’s-land a birnin Kano, bisa laifin fyaɗe.
Kotun ta bayar da umarnin a ci gaba da tsare shi, sannan ta ɗage ci gaba da sauraron ƙarar har zuwa ranar 9 ga watan Yunin 2026.















Discussion about this post