ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata A Bar Ƴansandan Jiha Ƙarƙashin Gwamnonin Jihohi Ba – Danbazau

by Sani Anwar
2 weeks ago
Jiha

Laftanar Janar Abdulrahman Dambazau, mai ritaya,  wanda tsohon babban hafsan soji ne, ya bayyana cewa; kafa ƴansandan jihohi, zai yi tasiri ne kaɗai a Nijeriya, idan aka tsaya aka yi abin da ya dace.

Dambazau, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) cewa; dole ne a killace ƴansandan jihohi daga hannun gwamnonin jihohi, domin hana kai wa ƴan adawar siyasarsu hari.

Ya kuma yi kira da kakkausar murya, wajen tantancewa tare da horar da ma’aikatan da za a ɗauka, domin tabbatar da cancanta da kuma daƙile munanan ɗabi’u.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, ya ƙara da cewa; dole ne tsarin ya haɗa da samar da daidaito da sa ido da kuma samar da ƙa’idojin aiki, domin hana yiwuwar cin zarafin bil’adama ko ɓullar ƙungiyoyin sa kai na ƙabilanci.

“Aikin yana buƙatar horarwa, kayan aiki, samar da horo, bayyana gaskiya, bin doka da oda da kuma mutunta haƙƙin Ɗan’adam.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

“Don haka, a duk inda ake da ƴansanda na jihohi da na ƙasa, idan ba a inganta ci gabansu ba, to ba za a samu sakamakon da ake buƙata ba.”

Ya ƙara da cewa, dangane da rashin tsaro, al’ummomin da aka fi kai wa hari, su ne yankunan karkara, ya ƙara da cewa; a waɗannan yankunan babu wani batun tabbatar da doka da oda a cikin al’umma.

“Wataƙila shi ya sa mutane ke kira ga ƴansandan jiha, amma babu shakka, aikin ƴansandan jiha, yana buƙatar abin da ƴansandan ƙasar ke buƙata.

“Na yi imanin cewa, mutane suna yin kira a kan hakan ne, saboda suna tunanin tsarin da muke da shi, don haka, idan an raba shi, zai yi aiki, eh, amma zai yi aiki ne kaɗai idan an kyautata shi, an yi abin da ya kamata.

“Idan an ɗauke shi, dole ne a horar da shi da kyau tare da tabbatar da cewa, akwai cikakkiyar ladabtarwa, kuma ana kula da jin daɗinsa yadda ya kamata.

“Dole ne ku tabbatar sun cika mafi ƙarancin ƙa’idojin aikin ƴansanda na duniya, babu shakka, bayan haka, dole ne ku tabbatar da cewa; akwai amana.

Dambazau, wanda yanzu shi ne jakadan Nijeriya da aka naɗa a ƙasar Sin, ya ce; “Wannan shi ya sa a wasu lokutan ma al’ummomi sukan bai wa ƴan fashi kuɗi don kare su daga wasu ƴan fashin.

Ya ƙara da cewa, “Don haka, babu shakka dole ne jihohin su kasance a shirye, domin samar da isassun kuɗaɗe.

Jiha
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Ƙasashen Afirka 10 Da Suka Fi Sayen Makaman Yaƙi

Ƙasashen Afirka 10 Da Suka Fi Sayen Makaman Yaƙi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.