ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata A Bar Ƴansandan Jiha Ƙarƙashin Gwamnonin Jihohi Ba – Danbazau

by Sani Anwar
2 months ago
Jiha

Laftanar Janar Abdulrahman Dambazau, mai ritaya,  wanda tsohon babban hafsan soji ne, ya bayyana cewa; kafa ƴansandan jihohi, zai yi tasiri ne kaɗai a Nijeriya, idan aka tsaya aka yi abin da ya dace.

Dambazau, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) cewa; dole ne a killace ƴansandan jihohi daga hannun gwamnonin jihohi, domin hana kai wa ƴan adawar siyasarsu hari.

Ya kuma yi kira da kakkausar murya, wajen tantancewa tare da horar da ma’aikatan da za a ɗauka, domin tabbatar da cancanta da kuma daƙile munanan ɗabi’u.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, ya ƙara da cewa; dole ne tsarin ya haɗa da samar da daidaito da sa ido da kuma samar da ƙa’idojin aiki, domin hana yiwuwar cin zarafin bil’adama ko ɓullar ƙungiyoyin sa kai na ƙabilanci.

“Aikin yana buƙatar horarwa, kayan aiki, samar da horo, bayyana gaskiya, bin doka da oda da kuma mutunta haƙƙin Ɗan’adam.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Don haka, a duk inda ake da ƴansanda na jihohi da na ƙasa, idan ba a inganta ci gabansu ba, to ba za a samu sakamakon da ake buƙata ba.”

Ya ƙara da cewa, dangane da rashin tsaro, al’ummomin da aka fi kai wa hari, su ne yankunan karkara, ya ƙara da cewa; a waɗannan yankunan babu wani batun tabbatar da doka da oda a cikin al’umma.

“Wataƙila shi ya sa mutane ke kira ga ƴansandan jiha, amma babu shakka, aikin ƴansandan jiha, yana buƙatar abin da ƴansandan ƙasar ke buƙata.

“Na yi imanin cewa, mutane suna yin kira a kan hakan ne, saboda suna tunanin tsarin da muke da shi, don haka, idan an raba shi, zai yi aiki, eh, amma zai yi aiki ne kaɗai idan an kyautata shi, an yi abin da ya kamata.

“Idan an ɗauke shi, dole ne a horar da shi da kyau tare da tabbatar da cewa, akwai cikakkiyar ladabtarwa, kuma ana kula da jin daɗinsa yadda ya kamata.

“Dole ne ku tabbatar sun cika mafi ƙarancin ƙa’idojin aikin ƴansanda na duniya, babu shakka, bayan haka, dole ne ku tabbatar da cewa; akwai amana.

Dambazau, wanda yanzu shi ne jakadan Nijeriya da aka naɗa a ƙasar Sin, ya ce; “Wannan shi ya sa a wasu lokutan ma al’ummomi sukan bai wa ƴan fashi kuɗi don kare su daga wasu ƴan fashin.

Ya ƙara da cewa, “Don haka, babu shakka dole ne jihohin su kasance a shirye, domin samar da isassun kuɗaɗe.

Jiha
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
Manyan Labarai

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Next Post
Ƙasashen Afirka 10 Da Suka Fi Sayen Makaman Yaƙi

Ƙasashen Afirka 10 Da Suka Fi Sayen Makaman Yaƙi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.