ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata A Bar Ƴansandan Jiha Ƙarƙashin Gwamnonin Jihohi Ba – Danbazau

by Sani Anwar
1 month ago
Jiha

Laftanar Janar Abdulrahman Dambazau, mai ritaya,  wanda tsohon babban hafsan soji ne, ya bayyana cewa; kafa ƴansandan jihohi, zai yi tasiri ne kaɗai a Nijeriya, idan aka tsaya aka yi abin da ya dace.

Dambazau, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) cewa; dole ne a killace ƴansandan jihohi daga hannun gwamnonin jihohi, domin hana kai wa ƴan adawar siyasarsu hari.

Ya kuma yi kira da kakkausar murya, wajen tantancewa tare da horar da ma’aikatan da za a ɗauka, domin tabbatar da cancanta da kuma daƙile munanan ɗabi’u.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, ya ƙara da cewa; dole ne tsarin ya haɗa da samar da daidaito da sa ido da kuma samar da ƙa’idojin aiki, domin hana yiwuwar cin zarafin bil’adama ko ɓullar ƙungiyoyin sa kai na ƙabilanci.

“Aikin yana buƙatar horarwa, kayan aiki, samar da horo, bayyana gaskiya, bin doka da oda da kuma mutunta haƙƙin Ɗan’adam.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

“Don haka, a duk inda ake da ƴansanda na jihohi da na ƙasa, idan ba a inganta ci gabansu ba, to ba za a samu sakamakon da ake buƙata ba.”

Ya ƙara da cewa, dangane da rashin tsaro, al’ummomin da aka fi kai wa hari, su ne yankunan karkara, ya ƙara da cewa; a waɗannan yankunan babu wani batun tabbatar da doka da oda a cikin al’umma.

“Wataƙila shi ya sa mutane ke kira ga ƴansandan jiha, amma babu shakka, aikin ƴansandan jiha, yana buƙatar abin da ƴansandan ƙasar ke buƙata.

“Na yi imanin cewa, mutane suna yin kira a kan hakan ne, saboda suna tunanin tsarin da muke da shi, don haka, idan an raba shi, zai yi aiki, eh, amma zai yi aiki ne kaɗai idan an kyautata shi, an yi abin da ya kamata.

“Idan an ɗauke shi, dole ne a horar da shi da kyau tare da tabbatar da cewa, akwai cikakkiyar ladabtarwa, kuma ana kula da jin daɗinsa yadda ya kamata.

“Dole ne ku tabbatar sun cika mafi ƙarancin ƙa’idojin aikin ƴansanda na duniya, babu shakka, bayan haka, dole ne ku tabbatar da cewa; akwai amana.

Dambazau, wanda yanzu shi ne jakadan Nijeriya da aka naɗa a ƙasar Sin, ya ce; “Wannan shi ya sa a wasu lokutan ma al’ummomi sukan bai wa ƴan fashi kuɗi don kare su daga wasu ƴan fashin.

Ya ƙara da cewa, “Don haka, babu shakka dole ne jihohin su kasance a shirye, domin samar da isassun kuɗaɗe.

Jiha
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
'Yan Bindiga
Manyan Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
Next Post
Ƙasashen Afirka 10 Da Suka Fi Sayen Makaman Yaƙi

Ƙasashen Afirka 10 Da Suka Fi Sayen Makaman Yaƙi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.