Laftanar Janar Abdulrahman Dambazau, mai ritaya, wanda tsohon babban hafsan soji ne, ya bayyana cewa; kafa ƴansandan jihohi, zai yi tasiri ne kaɗai a Nijeriya, idan aka tsaya aka yi abin da ya dace.
Dambazau, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) cewa; dole ne a killace ƴansandan jihohi daga hannun gwamnonin jihohi, domin hana kai wa ƴan adawar siyasarsu hari.
Ya kuma yi kira da kakkausar murya, wajen tantancewa tare da horar da ma’aikatan da za a ɗauka, domin tabbatar da cancanta da kuma daƙile munanan ɗabi’u.
Haka zalika, ya ƙara da cewa; dole ne tsarin ya haɗa da samar da daidaito da sa ido da kuma samar da ƙa’idojin aiki, domin hana yiwuwar cin zarafin bil’adama ko ɓullar ƙungiyoyin sa kai na ƙabilanci.
“Aikin yana buƙatar horarwa, kayan aiki, samar da horo, bayyana gaskiya, bin doka da oda da kuma mutunta haƙƙin Ɗan’adam.
“Don haka, a duk inda ake da ƴansanda na jihohi da na ƙasa, idan ba a inganta ci gabansu ba, to ba za a samu sakamakon da ake buƙata ba.”
Ya ƙara da cewa, dangane da rashin tsaro, al’ummomin da aka fi kai wa hari, su ne yankunan karkara, ya ƙara da cewa; a waɗannan yankunan babu wani batun tabbatar da doka da oda a cikin al’umma.
“Wataƙila shi ya sa mutane ke kira ga ƴansandan jiha, amma babu shakka, aikin ƴansandan jiha, yana buƙatar abin da ƴansandan ƙasar ke buƙata.
“Na yi imanin cewa, mutane suna yin kira a kan hakan ne, saboda suna tunanin tsarin da muke da shi, don haka, idan an raba shi, zai yi aiki, eh, amma zai yi aiki ne kaɗai idan an kyautata shi, an yi abin da ya kamata.
“Idan an ɗauke shi, dole ne a horar da shi da kyau tare da tabbatar da cewa, akwai cikakkiyar ladabtarwa, kuma ana kula da jin daɗinsa yadda ya kamata.
“Dole ne ku tabbatar sun cika mafi ƙarancin ƙa’idojin aikin ƴansanda na duniya, babu shakka, bayan haka, dole ne ku tabbatar da cewa; akwai amana.
Dambazau, wanda yanzu shi ne jakadan Nijeriya da aka naɗa a ƙasar Sin, ya ce; “Wannan shi ya sa a wasu lokutan ma al’ummomi sukan bai wa ƴan fashi kuɗi don kare su daga wasu ƴan fashin.
Ya ƙara da cewa, “Don haka, babu shakka dole ne jihohin su kasance a shirye, domin samar da isassun kuɗaɗe.















Discussion about this post