An sako fasinjoji 14 da aka sace a Jihar Benue bayan an biya kuɗin fansa kimanin Naira miliyan ɗaya.
Mutanen na cikin fasinjoji 16 da ke kan hanyarsu ta zuwa kudu maso yammacin Nijeriya lokacin da ‘yan bindiga suka kai musu hari a ranar 9 ga watan Fabrairu.
- Mutum 37 Sun Mutu, 25 Sun Jikkata Sakamakon Shaƙar Iskar Guba A Ramin Haƙar Ma’adinai A Filato
- Kudin Tikitin Kallon Fina-finai Yayin Hutun Bikin Bazara Na Kasar Sin Ya Zarce Yuan Biliyan 2
Mutane biyu sun mutu a harin.
Ƙungiyar matasa ta Igede ta tabbatar da sakinsu, inda ta ce iyalan waɗanda abin ya shafa sun tara Naira 500,000, yayin da ƙungiyar direbobi ta ƙara Naira 500,000 domin biyan kuɗin fansar.
Jami’an ƙananan hukumomi sun tabbatar da sakin mutanen amma ba su iya tabbatar da adadin kuɗin fansar da aka biya ba.
Haka kuma, rundunar ‘yansandan jihar ta ce har yanzu tana tattara bayanai.
Jami’ai sun buƙaci a ƙara tsaro a kan hanyar domin kare matafiya.















Discussion about this post