Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya amince da biyan tara domin sakin fursunoni sama da 90 da aka ɗaure kan ƙananan laifuffuka.
Gwamnatin jihar ta ce an ɗauki wannan mataki ne domin ba su damar yin sabuwar rayuwa, da kuma nuna tausayi da ake koyarwa a lokacin watan Ramadan.
- DSS Ta Kama El-Rufai Bayan EFCC Ta Bayar Da Belinsa
- Dokar Zaɓe: An Harba Barkonon Tsohuwa Ga Masu Zanga-zanga A Majalisa
An kuma buƙaci waɗanda aka saki su rungumi zaman lafiya, su bi doka, tare da bada gudummawa mai kyau ga al’umma.
ADVERTISEMENT
Gwamnan ya kuma roƙi mazauna jihar su yi amfani da wannan lokaci wajen aikata alheri, taimaka wa mabuƙata, tare da yin addu’a domin samun zaman lafiya da haɗin kai a jihar.















Discussion about this post