ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Tabbatar Da Ɓullar Cutar Apollo A Yobe Yayin Da Mazauna Yankin Ke Nuna Fargaba

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
Apollo

Asibitin Ƙwararru da ke Potiskum a Jihar Yobe ya tabbatar da ɓullar cutar ciwon ido ta ‘Acute hemorrhagic conjunctiɓitis’, da aka fi sani da (Apollo), yayin da fargaba ke ƙaruwa kan yadda cutar ke yaɗuwa a garin.

Asibitin ya ƙara da kiran mazauna yankin da su kiyaye tsaftar kai da ta muhalli, sannan su bi matakan kariya domin daƙile yaɗuwar cutar.

Shugaban kwamitin shawarwari kan harkokin lafiya na asibitin, Dr. Abubakar Sadiƙ Zakari, wanda ya wakilci Daraktan Asibitin, ya bayyana cewa cibiyar ta rubuta samun mutane da dama da suka kamu da cutar.

ADVERTISEMENT

To sai dai kuma, ya ce adadin mutanen da suka kamu na iya fin haka, kasancewar wasu ba sa zuwa asibiti sai dai su yi wa kansu magani a gida.

Zakari ya shawarci mazauna yankin da su riƙa wanke hannayensu akai-akai, su guji taɓa idanunsu, kuma su daina amfani da tawul, tufafi, kayan shimfiɗa, kofuna, ko sauran kayan amfanin yau da kullum tare da mutumin da ke da cutar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Haka zalika, ya yi kira ga mutanen da suka kamu da su rage haɗa jiki da mutane kuma su nufi asibiti da zarar sun fuskanci alamun cutar.

Kwamishinan Lafiya da Ayyukan Ajo na Jihar, Dr. Muhammad Lawan Gana, ya bayyana cewa ma’aikatar ta riga ta ƙarfafa matakan gaggawa domin ɗaƙile yaɗuwar cutar.

Ya ce an tsara muhimman saƙonni an rarraba su ga masu ruwa da tsaki da kafofin sada zumunta, sannan an umarci Jami’an Inganta Lafiya da su fahimtar da al’umma ta hanyar Masu Haɗa Kai na Ƙauyuka.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mazauna shiyya daban-daban a Potiskum sun ba da rahoton ƙaruwar mutanen da ke samun jajayen idanu ko kumburi da ƙaiƙayi da ciwo, da kuma fitar ruwa daga ido.

Wasu mazauna yankin sun bayyana cewa mutane da dama a gida guda sun kamu da cutar, lamarin da ke ƙara firgita jama’a kan saurin yaɗuwarta.

Wani mazaunin garin, Haladu Badejo, ya bayyana halin da ake ciki a matsayin mai ban tsoro, yana mai cewa cutar na yaɗuwa cikin sauri.

Wani mazaunin daban, Idris Bello Danchuawa, cewa ya yi: “Subhanallahi! Cutar Apollo (Ciwon Ido) tana ci gaba da yaɗuwa a Potiskum.”

Wani mai jinya, Abubakar Suleiman, ya bayyana cewa cutar ta zama babbar abin damuwa a garin.

“Wannan ciwon ido na Apollo ya zama kamar annoba a Potiskum. Rabonmu da mu ga cuta tana yaɗuwa haka tun daɗewa. Yana da wuya ka ziyarci gidaje biyu ba tare da ka tarar da wanda ya kamu da cutar ba,” in ji shi.

Suleiman ya ce cutar tana haifar da tsananin ja da ciwo a ido, ya kuma ƙara da cewa wasu marasa lafiyar sun sami sauƙi bayan amfani da ruwan ido (eye drops) da ƙwayoyin magani.

Apollo
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Apollo

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana 25 Ga Agusta Ranar Hutun Maulidi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.