ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Warware Rikicin Da Ya Bullo A Kungiyar Gwamnonin APC —Uba Sani

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
Uba sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce babu rikicin shugabanci a cikin kungiyar Gwamnonin APC ta Progressibe Gobernors’ Forum (PGF), yana mai jaddada cewa Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, har yanzu shi ne shugaban kungiyar.

PGF wata kafa ce da gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar APC ke amfani da ita wajen hada manufofi da karfafa hadin kai a cikin jam’iyyar mai mulki.

Sani, wanda shi ne mataimakin shugaban kungiyar, ya ce sabanin da ya kunno kai a cikin kungiyar gwamnonin APC kwanakin baya “karamin rashin fahimta ne” kawai wanda tuni aka warware.

ADVERTISEMENT

Gwamnan Kaduna ya bayyana hakan ne ranar Litinin yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels Telebision.

Kalaman nasa sun biyo bayan rahotannin da suka bayyana a makon da ya gabata cewa wai an cire Uzodimma daga shugabancin PGF tare da maye gurbinsa da Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, bayan wata ganawa mai zafi da aka yi a Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Rahotannin sun kuma yi ikirarin cewa kungiyar ta kasu gida biyu, inda wani bangare ke goyon bayan Uzodimma yayin da wani bangare ke mara wa Gwamnonin Dapo Abiodun na Ogun da Abdulrahman Abdulrazak na Kwara baya.

Lamarin ya haifar da hasashe kan yiwuwar rarrabuwar kai a cikin gwamnonin APC, inda aka ce Shugaba Bola Tinubu ya shiga tsakani domin kwantar da hankula tsakanin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

Sai dai Sani ya ce babu wani sauyin shugabanci a kungiyar, yana mai cewa dukkan gwamnoni sun sake haduwa.

Ya ce: “A ganina, ba babban al’amari ba ne kamar yadda wasu ke kokarin nuna shi.

“Saboda a dimokuradiyya mutane na iya yarda ko sabani da juna. Don haka a ganina karamin rashin fahimta ne kawai.

“A yanzu babu wata matsala. Dukkan gwamnoni suna tare. Mai girma Hope Uzodimma shi ne shugaban kungiyar Progressibe Gobernors Forum. Ni kuma, Sanata Uba Sani, ni ne mataimakin shugaban kungiyar,” in ji shi.

Sani ya bayyana cewa an warware matsalar gaba daya kuma ba za ta sake haifar da ce-ce-ku-ce ba.

“Ba na tunanin za ku sake jin wani abu game da wannan. Ina tabbatar muku, ba za ku sake jin wani abu ba,” in ji shi.

Da aka tambaye shi kai tsaye game da sabanin da ya faru a kungiyar, gwamnan Kaduna ya ce hakan abu ne da ya saba faruwa a siyasar dimokuradiyya.

“Abu ne na yau da kullum mutane su yi sabani. Amma kamar yadda na fada, wannan karamin rashin fahimta ne kawai, ba wani babban rikici bane, kuma an warware shi,” in ji shi.

Gwamnan ya kuma ce da ace da gaske an samu sauyin shugabanci, da shi ne zai karbi shugabancin kungiyar a matsayinsa na mataimakin shugaban kungiyar.

“Idan da akwai sauyin shugabanci, ni a matsayina na mataimakin shugaban kungiyar da na karbi shugabancin. Amma zan iya tabbatar muku cewa ni ina wurin, kuma ni ne na bayyana cewa muna hade kuma komai lafiya,” in ji Sani.

APC
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
kwankwaso

2027: Hadakar Obi Da Kwankwaso Na Shan Suka Daga Wasu Jagororin Siyasar Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.