ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Warware Rikicin Da Ya Bullo A Kungiyar Gwamnonin APC —Uba Sani

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago
Uba sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce babu rikicin shugabanci a cikin kungiyar Gwamnonin APC ta Progressibe Gobernors’ Forum (PGF), yana mai jaddada cewa Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, har yanzu shi ne shugaban kungiyar.

PGF wata kafa ce da gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar APC ke amfani da ita wajen hada manufofi da karfafa hadin kai a cikin jam’iyyar mai mulki.

Sani, wanda shi ne mataimakin shugaban kungiyar, ya ce sabanin da ya kunno kai a cikin kungiyar gwamnonin APC kwanakin baya “karamin rashin fahimta ne” kawai wanda tuni aka warware.

ADVERTISEMENT

Gwamnan Kaduna ya bayyana hakan ne ranar Litinin yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels Telebision.

Kalaman nasa sun biyo bayan rahotannin da suka bayyana a makon da ya gabata cewa wai an cire Uzodimma daga shugabancin PGF tare da maye gurbinsa da Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, bayan wata ganawa mai zafi da aka yi a Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Rahotannin sun kuma yi ikirarin cewa kungiyar ta kasu gida biyu, inda wani bangare ke goyon bayan Uzodimma yayin da wani bangare ke mara wa Gwamnonin Dapo Abiodun na Ogun da Abdulrahman Abdulrazak na Kwara baya.

Lamarin ya haifar da hasashe kan yiwuwar rarrabuwar kai a cikin gwamnonin APC, inda aka ce Shugaba Bola Tinubu ya shiga tsakani domin kwantar da hankula tsakanin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

Sai dai Sani ya ce babu wani sauyin shugabanci a kungiyar, yana mai cewa dukkan gwamnoni sun sake haduwa.

Ya ce: “A ganina, ba babban al’amari ba ne kamar yadda wasu ke kokarin nuna shi.

“Saboda a dimokuradiyya mutane na iya yarda ko sabani da juna. Don haka a ganina karamin rashin fahimta ne kawai.

“A yanzu babu wata matsala. Dukkan gwamnoni suna tare. Mai girma Hope Uzodimma shi ne shugaban kungiyar Progressibe Gobernors Forum. Ni kuma, Sanata Uba Sani, ni ne mataimakin shugaban kungiyar,” in ji shi.

Sani ya bayyana cewa an warware matsalar gaba daya kuma ba za ta sake haifar da ce-ce-ku-ce ba.

“Ba na tunanin za ku sake jin wani abu game da wannan. Ina tabbatar muku, ba za ku sake jin wani abu ba,” in ji shi.

Da aka tambaye shi kai tsaye game da sabanin da ya faru a kungiyar, gwamnan Kaduna ya ce hakan abu ne da ya saba faruwa a siyasar dimokuradiyya.

“Abu ne na yau da kullum mutane su yi sabani. Amma kamar yadda na fada, wannan karamin rashin fahimta ne kawai, ba wani babban rikici bane, kuma an warware shi,” in ji shi.

Gwamnan ya kuma ce da ace da gaske an samu sauyin shugabanci, da shi ne zai karbi shugabancin kungiyar a matsayinsa na mataimakin shugaban kungiyar.

“Idan da akwai sauyin shugabanci, ni a matsayina na mataimakin shugaban kungiyar da na karbi shugabancin. Amma zan iya tabbatar muku cewa ni ina wurin, kuma ni ne na bayyana cewa muna hade kuma komai lafiya,” in ji Sani.

APC
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
kwankwaso

2027: Hadakar Obi Da Kwankwaso Na Shan Suka Daga Wasu Jagororin Siyasar Kano

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.