Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce babu rikicin shugabanci a cikin kungiyar Gwamnonin APC ta Progressibe Gobernors’ Forum (PGF), yana mai jaddada cewa Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, har yanzu shi ne shugaban kungiyar.
PGF wata kafa ce da gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar APC ke amfani da ita wajen hada manufofi da karfafa hadin kai a cikin jam’iyyar mai mulki.
Sani, wanda shi ne mataimakin shugaban kungiyar, ya ce sabanin da ya kunno kai a cikin kungiyar gwamnonin APC kwanakin baya “karamin rashin fahimta ne” kawai wanda tuni aka warware.
Gwamnan Kaduna ya bayyana hakan ne ranar Litinin yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels Telebision.
Kalaman nasa sun biyo bayan rahotannin da suka bayyana a makon da ya gabata cewa wai an cire Uzodimma daga shugabancin PGF tare da maye gurbinsa da Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, bayan wata ganawa mai zafi da aka yi a Abuja.
Rahotannin sun kuma yi ikirarin cewa kungiyar ta kasu gida biyu, inda wani bangare ke goyon bayan Uzodimma yayin da wani bangare ke mara wa Gwamnonin Dapo Abiodun na Ogun da Abdulrahman Abdulrazak na Kwara baya.
Lamarin ya haifar da hasashe kan yiwuwar rarrabuwar kai a cikin gwamnonin APC, inda aka ce Shugaba Bola Tinubu ya shiga tsakani domin kwantar da hankula tsakanin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.
Sai dai Sani ya ce babu wani sauyin shugabanci a kungiyar, yana mai cewa dukkan gwamnoni sun sake haduwa.
Ya ce: “A ganina, ba babban al’amari ba ne kamar yadda wasu ke kokarin nuna shi.
“Saboda a dimokuradiyya mutane na iya yarda ko sabani da juna. Don haka a ganina karamin rashin fahimta ne kawai.
“A yanzu babu wata matsala. Dukkan gwamnoni suna tare. Mai girma Hope Uzodimma shi ne shugaban kungiyar Progressibe Gobernors Forum. Ni kuma, Sanata Uba Sani, ni ne mataimakin shugaban kungiyar,” in ji shi.
Sani ya bayyana cewa an warware matsalar gaba daya kuma ba za ta sake haifar da ce-ce-ku-ce ba.
“Ba na tunanin za ku sake jin wani abu game da wannan. Ina tabbatar muku, ba za ku sake jin wani abu ba,” in ji shi.
Da aka tambaye shi kai tsaye game da sabanin da ya faru a kungiyar, gwamnan Kaduna ya ce hakan abu ne da ya saba faruwa a siyasar dimokuradiyya.
“Abu ne na yau da kullum mutane su yi sabani. Amma kamar yadda na fada, wannan karamin rashin fahimta ne kawai, ba wani babban rikici bane, kuma an warware shi,” in ji shi.
Gwamnan ya kuma ce da ace da gaske an samu sauyin shugabanci, da shi ne zai karbi shugabancin kungiyar a matsayinsa na mataimakin shugaban kungiyar.
“Idan da akwai sauyin shugabanci, ni a matsayina na mataimakin shugaban kungiyar da na karbi shugabancin. Amma zan iya tabbatar muku cewa ni ina wurin, kuma ni ne na bayyana cewa muna hade kuma komai lafiya,” in ji Sani.















Discussion about this post