ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Warware Rikicin Da Ya Bullo A Kungiyar Gwamnonin APC —Uba Sani

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
Uba sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce babu rikicin shugabanci a cikin kungiyar Gwamnonin APC ta Progressibe Gobernors’ Forum (PGF), yana mai jaddada cewa Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, har yanzu shi ne shugaban kungiyar.

PGF wata kafa ce da gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar APC ke amfani da ita wajen hada manufofi da karfafa hadin kai a cikin jam’iyyar mai mulki.

Sani, wanda shi ne mataimakin shugaban kungiyar, ya ce sabanin da ya kunno kai a cikin kungiyar gwamnonin APC kwanakin baya “karamin rashin fahimta ne” kawai wanda tuni aka warware.

ADVERTISEMENT

Gwamnan Kaduna ya bayyana hakan ne ranar Litinin yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels Telebision.

Kalaman nasa sun biyo bayan rahotannin da suka bayyana a makon da ya gabata cewa wai an cire Uzodimma daga shugabancin PGF tare da maye gurbinsa da Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, bayan wata ganawa mai zafi da aka yi a Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Rahotannin sun kuma yi ikirarin cewa kungiyar ta kasu gida biyu, inda wani bangare ke goyon bayan Uzodimma yayin da wani bangare ke mara wa Gwamnonin Dapo Abiodun na Ogun da Abdulrahman Abdulrazak na Kwara baya.

Lamarin ya haifar da hasashe kan yiwuwar rarrabuwar kai a cikin gwamnonin APC, inda aka ce Shugaba Bola Tinubu ya shiga tsakani domin kwantar da hankula tsakanin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

Sai dai Sani ya ce babu wani sauyin shugabanci a kungiyar, yana mai cewa dukkan gwamnoni sun sake haduwa.

Ya ce: “A ganina, ba babban al’amari ba ne kamar yadda wasu ke kokarin nuna shi.

“Saboda a dimokuradiyya mutane na iya yarda ko sabani da juna. Don haka a ganina karamin rashin fahimta ne kawai.

“A yanzu babu wata matsala. Dukkan gwamnoni suna tare. Mai girma Hope Uzodimma shi ne shugaban kungiyar Progressibe Gobernors Forum. Ni kuma, Sanata Uba Sani, ni ne mataimakin shugaban kungiyar,” in ji shi.

Sani ya bayyana cewa an warware matsalar gaba daya kuma ba za ta sake haifar da ce-ce-ku-ce ba.

“Ba na tunanin za ku sake jin wani abu game da wannan. Ina tabbatar muku, ba za ku sake jin wani abu ba,” in ji shi.

Da aka tambaye shi kai tsaye game da sabanin da ya faru a kungiyar, gwamnan Kaduna ya ce hakan abu ne da ya saba faruwa a siyasar dimokuradiyya.

“Abu ne na yau da kullum mutane su yi sabani. Amma kamar yadda na fada, wannan karamin rashin fahimta ne kawai, ba wani babban rikici bane, kuma an warware shi,” in ji shi.

Gwamnan ya kuma ce da ace da gaske an samu sauyin shugabanci, da shi ne zai karbi shugabancin kungiyar a matsayinsa na mataimakin shugaban kungiyar.

“Idan da akwai sauyin shugabanci, ni a matsayina na mataimakin shugaban kungiyar da na karbi shugabancin. Amma zan iya tabbatar muku cewa ni ina wurin, kuma ni ne na bayyana cewa muna hade kuma komai lafiya,” in ji Sani.

APC
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Next Post
kwankwaso

2027: Hadakar Obi Da Kwankwaso Na Shan Suka Daga Wasu Jagororin Siyasar Kano

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.