Wani jigo a jam’iyyar APC ta Jihar Kano, Faizu Alfindiki, ya soki tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, kan abin da ya bayyana a matsayin kusancinsa da tafiyar siyasar tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi.
Da yake magana da manema labarai a Kano jiya, Alfindiki ya nuna shakku kan alkiblar siyasar Kwankwaso, yana zarginsa da kasa bai wa hadin kan Arewa muhimmanci a lokacin da yankin ke bukatar karin hadin kai tsakanin shugabannin siyasa.
Alfindiki, wanda tsohon shugaban karamar hukumar Kano Municipal ne, ya ce ‘yan Arewa da dama sun yi mamakin yadda Kwankwaso ya fi nuna sha’awar hada kai da bangaren Obi maimakon gina fahimta tsakanin manyan ‘yan siyasar Arewa masu tasiri.
A cewarsa, Arewa na bukatar karin hadin kai tsakanin fitattun ‘yan siyasar yankin domin kare muradun yankin da karfafa matsayinsa a siyasar kasa.
Ya ce: “Mutane da dama a Arewa suna kallon wannan mataki a matsayin rashin bai wa hadin kan yankin muhimmanci, musamman ganin cewa ana sa ran manyan shugabanni su fi mayar da hankali wajen hada kan Arewa da kare muradunta.”
Ya kuma yi zargin cewa Obi bai nuna damuwa kan manyan matsalolin Arewa ba, ciki har da rashin tsaro, noma da bunkasa tattalin arziki.
“Ba kasafai ake jin yana magana kan manyan kalubalen Arewa yadda mutane da dama ke tsammani daga wanda ke neman cikakken goyon bayan yankin ba,” in ji shi.
Alfindiki ya kuma yi zargin cewa rashin sha’awar Kwankwaso wajen yin aiki tare da sauran manyan ‘yan siyasar Arewa ya haifar da tunanin cewa muradinsa na siyasa ya fi karkata ga anfani na kai maimakon muradin yanki baki daya.
Ya ce: “A siyasa, ana auna mutum ne da matsayinsa da kuma irin hadin kan da yake ginawa. Mutanen Arewa na bukatar shugabanni da za su hada kai domin tabbatar da ci gaban yankin da kare martabarsa a siyasa.”
Sai dai ya yaba wa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu bisa abin da ya kira ayyukan ci gaba da ake gani a fadin Arewa, musamman a fannoni kamar gine-ginen more rayuwa, tituna da noma.















Discussion about this post