ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yanke Wa Dan Kungiyar Asiri Hukuncin Kisa A Ekiti

by Sadiq
4 years ago
Ekiti

Wata babbar kotun Jihar Ekiti da ke zamanta a Ado Ekiti, ta yanke wa wani Segun Iwaetan hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa samunsa da laifin zama dan kungiyar asiri da kuma laifin yi wa budurwa ‘yar shekara 20 fyade.

Kotun ta yanke wa matashin mai shekaru 24 hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa samunsa da laifin yi wa makwabciyarsa fyade, waadda dalibar Kwalejin Fasaha ta Ado Ekiti ce.

  • An Fitar Da Rahoton Masana Kan Ra’ayin Kare Hakkin Dan Adam Na Sin
  • 2023: Buhari Ya Hori Jami’an Tsaro Su Zama ‘Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

An gurfanar da Iwaetan akan tuhume-tuhume bakwai da suka shafi fyade, mallakar makamai ba bisa ka’ida ba, da shiga kungiyar asiri, da sauran laifuka.

ADVERTISEMENT

A cewar tuhumar, “Segun Iwaetan da Atila Iwaetan (a halin yanzu) a ranar 16 ga Janairu, 2021, sun hada baki wajen yin sata, sun shiga shagon wani Olayemi Oyerinde, sun karbi kadarori irin su rigar polo 15, wando jean 50, silifas na fata guda 30 da dai sauransu, wanda ya kai sama da Naira miliyan 1.8.

“A ranar 5 ga watan Fabrairu, 2021, Iwaetan ya yi wa wata daliba ‘yar shekara 20 fyade a Titin Odo Ado, Ado Ekiti, yayin da ya mallaki bindigogi biyu ba bisa ka’ida ba. An same shi, a ranar 10 ga watan Fabrairu, 2021 da kasancewa memba na kungiyar asiri ta ”

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

‘Eiye confraternity’,” in ji shi.

Wadda aka yi wa fyaden a cikin shaidar ta, ta bayyana cewa, “A ranar, wadda ake kara ya samu shiga dakina da misalin karfe 3 na dare, kuma ya nuna min bindiga yayin da ya umarce ni da kada in yi ihu idan ba haka ba ya harbe ni.

“Ya umarce ni da in cire kayana kuma ya yi lalata da ni ta karfin tsiya.

“a lokacin da ya yi min fyade, har yanzu ni budurwa ce. Bayan haka, ya roke ni gafara kuma ya ce kada in gaya wa kowa game da lamarin.”

Lauyan mai gabatar da kara, Albert Adeyemi, ya kira shaidu biyar sannan ya gabatar da bayanin wanda ake kara, sammacin bincike, bindigogi biyu na gida a matsayin shaida da kuma rahoton likita.

Mai shari’a Adeniyi Familoni, wanda ke yanke hukuncin, ya yanke wa wanda ake kara hukunci a kan tuhume-tuhume hudu.

Alkalin ya ce, “An yanke wa wanda ake tuhuma hukuncin kamar haka: hada baki da mallakar makamai ba bisa ka’ida ba, an yanke masa hukuncin daurin shekaru 12 a gidan yari kowane ba tare da wani zabin biyan tara ba, za a ci gaba da zartar da hukunci a lokaci guda daga ranar da aka kama shi da kuma tsare wanda ake tuhuma.

“Akan fyade, kotu ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai ga wanda ake kara,” yayin da saboda kasancewa memba na kungiyar asiri ta Eiye confraternity, alkali ya shaida wa wanda ake kara cewa, “Hukuncin da wannan kotu ta yanke a kan ku shi ne a rataye shi har sai kun mutu.”

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
Rahotonni

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
Labarai

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Next Post
Mayakan ISWAP Da Boko Haram Sun Tafka Kazamin Fada A Tsakaninsu

Mayakan ISWAP Da Boko Haram Sun Tafka Kazamin Fada A Tsakaninsu

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.