Wani shaharren magoya bayan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu mai suna Alhaji Sani Ahmad Zangina ya bayyana cewa ‘yan siyasan da suke yin tawaye bayan sun kasa samun tikitin yin takara a zabubbkan fidda gwani da jam’iyyar APC ta gudanar a sassan kasar nan da cewa, ba cikakkun masu kishin jam’iyyar ba ne kuma ba cikakkun masu kisin kasa ba ne.
Alhaji Zangina tattauna ne da manema labarai a a ofishinsa da ke Abuja, ya kuma bayar da misali da yadda tsohon ministan sadarwa Farfesa Ali Isa Pantami wanda ya nemi takarar kujerar gwamnan Jihar Gombe a jam’iyyar APC amma bai samu nasara ba a zaben da aka yi inda Alhaji Ishaku Jamilu Gwamna ya samu amincewar ‘yan jami’iyyar a zaben da aka yi, amma maimakon ya rungumi kaddara ya hada hannu da sauran ‘yan jam’iyyar domin fuskantar yadda za a samu nasara a babbar zaben da ke tafe sai kawai ya yi tawaye, har ya sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP inda bayanai ke nuna cewa har sun bashi tikitin takarar kujerar gwamna.
Ya kara da cewa, ya kamata ‘yan siyasa su fahimci cewa, duk wata kujerar da aka yi takara mutum daya ne zai dare, saboda haka ya kamata sauran ‘yan jam’iyyar su hada hannu don goya wa wanda ya samu nasara baya domin nasarar jam’iyyar shi ne babbar burin duk wani mai kishin jam’iyya.
Ya kuma kara dea cewa, “Wadannan mutane ne da APC ta rufa wa asiri a rayuwar su ta hanyar basu mukamai a lokutta daban-dabban, sai yanzu saboda sun rasa nasarar cin zabe sai su yi tawaye, wannan ba halin ‘yan siyasan kirki ba ne”.
Daga karshe ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi watsi da kiraye-kirayen ‘yan adawa su tabbatar da sun zabi Shugaba Tinubu domin ya ci gaba da ayyukan raya kasa da ya fara. Ya kuma jinjina wa jami’an tsaro a ayyukan tabbatar da yaki da ‘yan ta’adda da suke yi, ya kuma bukaci al’umma su jajirce wajen bayar da muhimman bayanan sirri na ayyukan ‘yan ta’adda ga jami’an tsaronmu donmin samun nasarar aikin da suke yi.














Discussion about this post