Haɗin gwuiwar jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji, ‘yansanda da ‘yan banga ya yi nasarar cafke mutane huɗu da ake zargi da garkuwa da mutane tare da ceto wata mata da ɗanta da aka sace a ƙaramar hukumar Alkaleri ta jihar Bauchi.
Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, SP Nafiu Habib, ya ce an kama wasu daga cikin waɗanda ake zargin a ƙauyen Kuka da ke gundumar Duguri bayan wani sumame da aka gudanar bisa sahihan bayanan sirri. Ya ce bincike ya fara ne bayan maharan sun sace wata mata mai shekaru 40 da ɗanta mai shekaru 25 daga unguwar Kwarin Gadali da ke gundumar Pali.
A cewarsa, binciken ya kai ga kama wasu daga cikin waɗanda ake zargi, waɗanda suka bayar da bayanan da suka taimaka wajen gano inda aka ɓoye waɗanda aka sace. Daga bisani jami’an tsaro suka ceto mutanen biyu ba tare da sun ji rauni ba, sannan aka kai su babban asibitin Alkaleri domin duba lafiyarsu.
Rundunar ta ce an miƙa binciken lamarin ga sashin yaƙi da garkuwa da mutane, yayin da ake ci gaba da farautar sauran waɗanda suka tsere. Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya yaba da aikin jami’an tsaro tare da yin kira ga jama’a su ci gaba da bai wa hukumomi sahihan bayanai domin yaƙar laifuffuka.















Discussion about this post