ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Samun Nasara A Yaƙi Da Cutar Fuka Da Kuturta A Jihar Zamfara

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
Zamfara

Shirin Kula da Cutar Tarin Fuka, Kuturta da Buruli Ulcer na Jihar Zamfara ya samu gagarumar nasara wajen gano cututtuka, kula da marasa lafiya da kuma rigakafi.

An bayyana wannan nasara ce a yayin taron bitar aiki na kowane kwata da aka yi da ƙungiyoyin ƙananan hukumomi a Fulbe Villa Hotel, Gusau, babban birnin Jihar Zamfara.

  • Zamfara: PDP Ta Yaba Wa Kotun Abuja Kan Nasarar Da Ta Samu
  • Gwamnatin Zamfara Ta Ɓullo Da Shirin Amfana Da Ma’adanai Ga Al’umma Jihar

Taron ya haɗa jami’an shirin, masu kula da tarin fuka a ƙananan hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki domin nazartar ci gaba da kuma inganta ayyukan ba da lafiya.

ADVERTISEMENT

Kwamishinar Lafiya ta Jihar Zamfara, Nafisa Muhammad Maradun, ta ce shirin ya ƙara ƙaimi wajen neman masu cutar a dukkan matakan kula da lafiya, lamarin da ya kai ga samun kashi 99 cikin 100 na nasarar jinya da kuma rajistar kashi 100 cikin 100 ga duk marasa lafiyar da aka gano.

“Bayanan da muka tattara sun nuna ƙarin kashi 27 cikin 100 na gano sabbin masu cutar tarin fuka a shekarar 2025 idan aka kwatanta da 2024. Haka kuma, gano tarin fuka a cikin yara ya ƙaru da kashi 47 cikin 100 a wannan lokaci,” in ji Kwamishiniyar.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Shirin ya kuma raba motocin aiki da babura domin tallafa wa sa ido, bibiyar ayyuka da kuma wayar da kai a cikin al’umma, tare da gudunmawar masu tallafa wa shirin.

Dr. Nafisa Maradun ta ce ƙarfafa haɗin gwiwa da abokan hulɗa ya taimaka matuƙa wajen tabbatar da aiwatar da ayyukan shirin yadda ya kamata a faɗin jihar.

“Daga zangon uku na shekarar 2024 zuwa zangon biyu na 2025, an yi wa marasa lafiya 8,891 rajista domin jinya, inda 4,769 maza ne, yayin da 4,122 mata ne. Daga cikinsu, 8,802 sun warke kuma sun kammala jinyarsu, wanda ya nuna kashi 99 cikin 100 na nasarar jinya.

Adadin mutuwa ya tsaya a kashi 0.7 cikin 100, yayin da waɗanda suka daina jinya suka kai kashi 0.3 cikin 100,” in ji ta.

Kwamishinar ta ƙara da cewa a cikin wannan lokaci, an tantance mutum 404,098 domin cutar tarin fuka, inda 125,935 ake tunanin da yiwuwar za su ɗauki cutar, sannan 10,006 aka tabbatar da suna da cutar.

Zamfara
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Mika Ma’aikatan Wani Jirgin Ruwa 17 Da Ta Ceto Ga Kasar Philippines

Kasar Sin Ta Mika Ma’aikatan Wani Jirgin Ruwa 17 Da Ta Ceto Ga Kasar Philippines

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.