Gwamnatin Jihar Zamfara ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal ta vullo da shirin amfana da ma’adanai ga al’ummar jihar.
Kwamishinan mahalli da albarkacin ƙasa na jihar, Hon Kasimu Sani Kaura ne ya bayyana haka a lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai a Gusau, babban birnin jihar.
Hon Kasimu ya bayyana cewa Gwamna Dauda ya ziyarci inda ake haƙar ma’adanai ba tare da izini ba a yankin Maru, don ganin yadda ɗaruruwan mutane ke haƙar ma’adanai. Gwamna Dauda ya yi masu cikakken bayani, inda ya bayyana cewa ba za a hana su cin gajiyar ma’adanan da Allah ya azirta jihar da su ba, amma ya kamata su yi ƙungiyoyi da amincewar sarakunansu su tantace kawunansu ko kuma su kawo mana don a yi masu rajista kamar yadda doka ta tanada.
- Jami’an Tsaro 6 Sun Rasu Yayin Da Aka Daƙile Harin ’Yan Ta’adda A Zamfara
- Zamfara: PDP Ta Yaba Wa Kotun Abuja Kan Nasarar Da Ta Samu
Ya ce, “Ku yi aikinku cikin kwanciyar hankali da lumana. Kuma da yardar Allah za mu taimaka maku wajan ganin kun samu rajista ta jihar da kuma ta gwamnatin tarayya,” in ji Gwamna Dauda.
Hon Kasimu ya kuma tabbatar da cewa tuni ma’aikatar ma’adanai ta soma shirin haɗa kan ƙungiyoyin don ganin al’umma sun amfani da arziki da Allah ya hore wa jihar.
Kwamishinan ya yi kira ga al’ummar Jihar Zamfara da su bi umarnan Gwamna Dauda wajen samar da ƙungiyoyin ta hannun sarakuna bisa tsaro kamar yadda doka ta tanada.














Discussion about this post