ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Farashi

Yayin da bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara ke gabatowa, farashin kayan abinci kamar shinkafa, garri da doya sun ragu sosai a fadin ƙasar.

Yawancin kayan abinci ya yi tsada ne sakamakon cire tallafin man fetur da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi a 2023 da kuma rashin tsaro a yankunan da ake noma; duk da haka, binciken da LEADERSHIP Weekend ta gudanar ya nuna cewa yawancin farashin kayan abincin sun sauka.

  • Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas
  • Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

Yanayin bukukuwan na kawo farin ciki da dan tashin hankali a kasuwa saboda yawan jama’ar da ke yin tururuwar sayen kayayyaki iri daya a lokaci guda.

ADVERTISEMENT

Lokacin da LEADERSHIP Weekend ta ziyarta kasuwannin Relief da World Bank a Jihar Imo, buhun shinkafa kilo kigiram 50 da ake sayarwa Naira 75,000 yanzu ana sayar da shi a Naira 60,000.

Guga 10 na garri da ake sayarwa a Naira 7,600 a watan Nuwamba yanzu ya koma N5,000. Haka kuma, kashin doya da ake saye a Naira 2,500 yanzu ana samun sa a Naira 1,900, yayin da buhun wake na kili giram 50 da ake saya a Naira 34,000 a baya, yanzu ana sayar da shi a Naira 30,000.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

 

A Legas farashin shinkafa ya fadi sosai

A kasuwannin Mushin da Daleko, farashin buhun shinkafa kilo 50 da ake sayar da shi a da Naira N75,000 cikin Nuwamba, a yanzu ya dawo Naira 54,000.

 

Jihar Delta

A Jihar Delta, musamman a Asaba, farashin kayan abinci ya daidaita a manyan kasuwanni irin su Kasuwar Oko (Hausa), Midwifery Market da Ogbogonogo Market, sai dai a kasuwannin mako-mako na kauyuka.

Bincike a babban birnin jihar ya nuna cewa farashin muhimman kayan abinci ya dan daidaita, amma ‘yan kasuwa da masu sayayya sun nuna damuwa kan karancin kudin da ake da shi don sayayya.

Kwandon tumatir da ake sayarwa Naira 5,000 a wasu watanni da suka gabata, yanzu ya sakko Naira 4,000. Farashin doya ya tsaya a tsakanin Naira 1,800 zuwa Naira 2,000 kowace guda, yayin da garri yake kan Naira 3,000 gwangwani, ba tare da sauyi ba duk da lokacin girbi.

A Kasuwar Ogbogonogo, wata mai girki, Mrs Beatrice Nnamdi, ta ce wasu kayan abinci har yanzu suna da tsada duk da zuwan sabbin kayan abinci.

“Talon shinkafa yanzu yana tsakanin Naira 60,000 zuwa Naira 65,000. A da yana tsakanin Naira 90,000 zuwa Naira120,000. Buhun wake yanzu Naira 50,000. Mun taba sayarwa a nan tsakanin Naira70,000 zuwa Naira 90,000,” in ji ta.

“A lokacin girbi, idan doya, masara da dankali suka fara fitowa, ya kamata garri ya yi sauki. Tumatir yanzu yana tsakanin Naira 7,500 zuwa Naira 8,000, gwangwani Wake da shinkafa sun sauka kadan daga Naira 6,000 zuwa Naira 5,500 gwangwani,” a cewarta.

 

Jihar Yobe

Manoma a wasu sassan Jihar Yobe, musamman a cikin da kewaye da Damaturu, babban birnin jihar, na fama da mummunan tasirin fari wanda ya busar da amfanin gona saboda karancin ruwan sama.

Da dama daga cikin manoma da mazauna yankunan da abin ya shafa sun bayyana fargaba matuka game da karancin ruwan sama a bana, wanda suka ce ya rage girbinsu kuma ya kara tsananta yanayin rayuwarsu.

Wasu daga cikin manoman sun shaida wa LEADERSHIP Weekend cewa karancin ruwan sama a wannan yanki, idan aka kwatanta da wasu sassan jihar da suka samu isasshen ruwan sama, ya sa amfanin gona irin su masara, gero da shinkafa suka bushe, kuma hakan na iya jawo karancin abinci a gaba.

Daya daga cikin manoman, Mallam Bukar Abba, mazaunin Damaturu, ya ce fari da ya biyo bayan karancin ruwan sama ya bar amfanin gona suna bushewa.

Bukar ya ce ruwan sama ya tsaya da wuri, kuma lokutan da ya yi, zuba yayyafi ne kawai ba wanda zai wadatar don ciyar da amfanin gona ba.

Ya kara da cewa ruwan saman bana ya bar manoma da fargabar tsaro a fannin abinci, inda ya nuna cewa da dama daga cikin manoma sun yi asarar miliyoyin naira saboda amfanin gonar bai kai lokacin girma ba kafin ya bushe.

Wani manomin da ke kuka da halin fari, Mohammed Salisu, mazaunin Karamar Hukumar Gashua, ya ce karancin ruwan saman ya yi mummunan tasiri sosai domin ya lalata hanyar samun rayuwarsu.

 

Jihar Kaduna

A Kaduna, wani mai sayar da kayan abinci na Kasuwar Sabon Tasha, Elias Samson, ya ce farashin kayan abinci ya ci gaba da daidaituwa tun bayan da gwamnatin tarayya ta rage farashin abinci.

“Farashin abinci yana fara tashi ne a watan Disamba, kusa da Kirsimeti, amma a halin yanzu farashin yana nan yadda yake. Ka san manoma har yanzu suna girbe masara, wake, shi ya sa ake da tsoffin kayan abinci da sababbi a kasuwa yanzu. A lokacin girbi farashi ba ya tashi haka kawai,” in ji shi.

Wata mai sayen kayan abinci, Laadi Onoja, ta ce: “Farashin abinci har yanzu yana da kyau idan aka kwatanta da yadda muke saya wasu watanni da suka gabata. Lokacin cunkoso shi ne watan Disamba, kuma a wancan lokacin wasu dillalai kan kara kudi domin samun karin riba.

Na sayi mudu daya na shinkafa mai tsabta Naira 1,800 kuma wasu wurare suna sayarwa Naira 1,700 musamman a kasuwannin kauye.”

 

Jihar Kogi

An samu daidaituwar farashin kayan abinci a Lokoja, babban birnin Jihar Kogi, matuka, ban da naman Sa wanda ya rika tashi a ‘yan watannin nan.

Lokacin da LEADERSHIP Weekend ta ziyarci sabuwar kasuwa a Lokoja, ana sayar da shinkafa Naira 7,000 maimakon farashin da ya kai Naira 14,500 a da.

Wata ‘yar kasuwa mai sayar da shinkafa da wake, Hajiya Lami Sule, ta ce babu wani tashin farashi da aka samu kan kayan abinci.

Sai dai a wajen sayar da nama, lamari ya bambanta domin farashin kilo daya na nama yana kara tashi kullum.

Wani mutum mai matsakaicin shekaru, Ismail Jegede, ya ce: “Ban da farashin nama, farashin sauran kayan abinci ya yi tsaya dai-dai a kasuwannin baya guda biyar. Kilo daya na nama da muke saya tsakaninNaira 3,500 zuwa Naira 4,500 yanzu ana sayar da shi Naira 6,000.”

Shi ma wani mai sayar da nama a sabuwar kasuwar Lokoja, Mallam Danladi Abu, ya danganta tashin farashin namansa ga kudin sufuri da kuma matsalar tsaro.

“Dole mu je wurare masu nisa domin samun shanu saboda rashin tsaro. Mafi nisan wurin da muka tafi, shi ne mafi tsadar jigilar dabbar,” in ji shi.

 

Jihar Akwa Ibom

A yayin haka, farashin yawancin kayan abinci na yau da kullum, kamar garri, wake, shinkafa, albasa, barkono da sauran su, ya kasance daidai, a cewar binciken da aka gudanar a manyan kasuwanni a Uyo, da kuma Kananan Hukumomin Itu da Etinan.

Kodayake har yanzu ya yi wuri a yi hasashen abin da zai faru domin har yanzu jihar ba ta fuskanci cunkoson jama’ar bukukuwan shekara ba, farashin kayayyaki ya kasance a daidaitacce a kasuwannin Akpan Andem Market (Uyo), Itam International Market (Itu) da Okpokpo Market (Etinan).

Garri, wanda a baya ake sayar da kofi 5 zuwa 6 kan Naira 1,000 bayan shugaba Tinubu ya hau mulki, yanzu ana samun kofuna 12 zuwa 13 akan farashi guda.

Buhun shinkafa, da a baya yake tsakanin Naira 70,000 zuwa Naira 80,000, yanzu yana tsakanin Naira 38,000, Naira 47,000 zuwa Naira 60,000 gwargwadon inganci da nau’in hatsi.

Farashin wake ya sauka daga Naira 450 zuwa Naira 500 zuwa Naira 250 zuwa Naira 300.

Naman Sa kuwa ya ci gaba da kasancewa mai tsada tsakanin Naira 3,000 zuwa Naira 3,200 kowane kilo, yayin da farashin kaji ya sauka daga Naira 10,000 zuwa Naira 15,000 zuwa Naira 6,000.

Wani dillalin hatsi daga Sokoto, Adamu Isa, ya danganta saukar farashin da matakin da gwamnatin Jihar Akwa Ibom ta dauka na rusa kungiyoyin kasuwa a manyan kasuwanni.

Wani dillalin dabbobi, Abubakar Garba, ya bayyana cewa matakin Gwamnonin Nijeriya (NGF) na kawar da harajin kan tituna toll points “shima babban dalili ne da ya taimaka wajen rage farashin muhimman kayan masarufi.”

Farashi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post

Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.