ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
Farashi

Yayin da bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara ke gabatowa, farashin kayan abinci kamar shinkafa, garri da doya sun ragu sosai a fadin ƙasar.

Yawancin kayan abinci ya yi tsada ne sakamakon cire tallafin man fetur da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi a 2023 da kuma rashin tsaro a yankunan da ake noma; duk da haka, binciken da LEADERSHIP Weekend ta gudanar ya nuna cewa yawancin farashin kayan abincin sun sauka.

  • Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas
  • Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

Yanayin bukukuwan na kawo farin ciki da dan tashin hankali a kasuwa saboda yawan jama’ar da ke yin tururuwar sayen kayayyaki iri daya a lokaci guda.

ADVERTISEMENT

Lokacin da LEADERSHIP Weekend ta ziyarta kasuwannin Relief da World Bank a Jihar Imo, buhun shinkafa kilo kigiram 50 da ake sayarwa Naira 75,000 yanzu ana sayar da shi a Naira 60,000.

Guga 10 na garri da ake sayarwa a Naira 7,600 a watan Nuwamba yanzu ya koma N5,000. Haka kuma, kashin doya da ake saye a Naira 2,500 yanzu ana samun sa a Naira 1,900, yayin da buhun wake na kili giram 50 da ake saya a Naira 34,000 a baya, yanzu ana sayar da shi a Naira 30,000.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

 

A Legas farashin shinkafa ya fadi sosai

A kasuwannin Mushin da Daleko, farashin buhun shinkafa kilo 50 da ake sayar da shi a da Naira N75,000 cikin Nuwamba, a yanzu ya dawo Naira 54,000.

 

Jihar Delta

A Jihar Delta, musamman a Asaba, farashin kayan abinci ya daidaita a manyan kasuwanni irin su Kasuwar Oko (Hausa), Midwifery Market da Ogbogonogo Market, sai dai a kasuwannin mako-mako na kauyuka.

Bincike a babban birnin jihar ya nuna cewa farashin muhimman kayan abinci ya dan daidaita, amma ‘yan kasuwa da masu sayayya sun nuna damuwa kan karancin kudin da ake da shi don sayayya.

Kwandon tumatir da ake sayarwa Naira 5,000 a wasu watanni da suka gabata, yanzu ya sakko Naira 4,000. Farashin doya ya tsaya a tsakanin Naira 1,800 zuwa Naira 2,000 kowace guda, yayin da garri yake kan Naira 3,000 gwangwani, ba tare da sauyi ba duk da lokacin girbi.

A Kasuwar Ogbogonogo, wata mai girki, Mrs Beatrice Nnamdi, ta ce wasu kayan abinci har yanzu suna da tsada duk da zuwan sabbin kayan abinci.

“Talon shinkafa yanzu yana tsakanin Naira 60,000 zuwa Naira 65,000. A da yana tsakanin Naira 90,000 zuwa Naira120,000. Buhun wake yanzu Naira 50,000. Mun taba sayarwa a nan tsakanin Naira70,000 zuwa Naira 90,000,” in ji ta.

“A lokacin girbi, idan doya, masara da dankali suka fara fitowa, ya kamata garri ya yi sauki. Tumatir yanzu yana tsakanin Naira 7,500 zuwa Naira 8,000, gwangwani Wake da shinkafa sun sauka kadan daga Naira 6,000 zuwa Naira 5,500 gwangwani,” a cewarta.

 

Jihar Yobe

Manoma a wasu sassan Jihar Yobe, musamman a cikin da kewaye da Damaturu, babban birnin jihar, na fama da mummunan tasirin fari wanda ya busar da amfanin gona saboda karancin ruwan sama.

Da dama daga cikin manoma da mazauna yankunan da abin ya shafa sun bayyana fargaba matuka game da karancin ruwan sama a bana, wanda suka ce ya rage girbinsu kuma ya kara tsananta yanayin rayuwarsu.

Wasu daga cikin manoman sun shaida wa LEADERSHIP Weekend cewa karancin ruwan sama a wannan yanki, idan aka kwatanta da wasu sassan jihar da suka samu isasshen ruwan sama, ya sa amfanin gona irin su masara, gero da shinkafa suka bushe, kuma hakan na iya jawo karancin abinci a gaba.

Daya daga cikin manoman, Mallam Bukar Abba, mazaunin Damaturu, ya ce fari da ya biyo bayan karancin ruwan sama ya bar amfanin gona suna bushewa.

Bukar ya ce ruwan sama ya tsaya da wuri, kuma lokutan da ya yi, zuba yayyafi ne kawai ba wanda zai wadatar don ciyar da amfanin gona ba.

Ya kara da cewa ruwan saman bana ya bar manoma da fargabar tsaro a fannin abinci, inda ya nuna cewa da dama daga cikin manoma sun yi asarar miliyoyin naira saboda amfanin gonar bai kai lokacin girma ba kafin ya bushe.

Wani manomin da ke kuka da halin fari, Mohammed Salisu, mazaunin Karamar Hukumar Gashua, ya ce karancin ruwan saman ya yi mummunan tasiri sosai domin ya lalata hanyar samun rayuwarsu.

 

Jihar Kaduna

A Kaduna, wani mai sayar da kayan abinci na Kasuwar Sabon Tasha, Elias Samson, ya ce farashin kayan abinci ya ci gaba da daidaituwa tun bayan da gwamnatin tarayya ta rage farashin abinci.

“Farashin abinci yana fara tashi ne a watan Disamba, kusa da Kirsimeti, amma a halin yanzu farashin yana nan yadda yake. Ka san manoma har yanzu suna girbe masara, wake, shi ya sa ake da tsoffin kayan abinci da sababbi a kasuwa yanzu. A lokacin girbi farashi ba ya tashi haka kawai,” in ji shi.

Wata mai sayen kayan abinci, Laadi Onoja, ta ce: “Farashin abinci har yanzu yana da kyau idan aka kwatanta da yadda muke saya wasu watanni da suka gabata. Lokacin cunkoso shi ne watan Disamba, kuma a wancan lokacin wasu dillalai kan kara kudi domin samun karin riba.

Na sayi mudu daya na shinkafa mai tsabta Naira 1,800 kuma wasu wurare suna sayarwa Naira 1,700 musamman a kasuwannin kauye.”

 

Jihar Kogi

An samu daidaituwar farashin kayan abinci a Lokoja, babban birnin Jihar Kogi, matuka, ban da naman Sa wanda ya rika tashi a ‘yan watannin nan.

Lokacin da LEADERSHIP Weekend ta ziyarci sabuwar kasuwa a Lokoja, ana sayar da shinkafa Naira 7,000 maimakon farashin da ya kai Naira 14,500 a da.

Wata ‘yar kasuwa mai sayar da shinkafa da wake, Hajiya Lami Sule, ta ce babu wani tashin farashi da aka samu kan kayan abinci.

Sai dai a wajen sayar da nama, lamari ya bambanta domin farashin kilo daya na nama yana kara tashi kullum.

Wani mutum mai matsakaicin shekaru, Ismail Jegede, ya ce: “Ban da farashin nama, farashin sauran kayan abinci ya yi tsaya dai-dai a kasuwannin baya guda biyar. Kilo daya na nama da muke saya tsakaninNaira 3,500 zuwa Naira 4,500 yanzu ana sayar da shi Naira 6,000.”

Shi ma wani mai sayar da nama a sabuwar kasuwar Lokoja, Mallam Danladi Abu, ya danganta tashin farashin namansa ga kudin sufuri da kuma matsalar tsaro.

“Dole mu je wurare masu nisa domin samun shanu saboda rashin tsaro. Mafi nisan wurin da muka tafi, shi ne mafi tsadar jigilar dabbar,” in ji shi.

 

Jihar Akwa Ibom

A yayin haka, farashin yawancin kayan abinci na yau da kullum, kamar garri, wake, shinkafa, albasa, barkono da sauran su, ya kasance daidai, a cewar binciken da aka gudanar a manyan kasuwanni a Uyo, da kuma Kananan Hukumomin Itu da Etinan.

Kodayake har yanzu ya yi wuri a yi hasashen abin da zai faru domin har yanzu jihar ba ta fuskanci cunkoson jama’ar bukukuwan shekara ba, farashin kayayyaki ya kasance a daidaitacce a kasuwannin Akpan Andem Market (Uyo), Itam International Market (Itu) da Okpokpo Market (Etinan).

Garri, wanda a baya ake sayar da kofi 5 zuwa 6 kan Naira 1,000 bayan shugaba Tinubu ya hau mulki, yanzu ana samun kofuna 12 zuwa 13 akan farashi guda.

Buhun shinkafa, da a baya yake tsakanin Naira 70,000 zuwa Naira 80,000, yanzu yana tsakanin Naira 38,000, Naira 47,000 zuwa Naira 60,000 gwargwadon inganci da nau’in hatsi.

Farashin wake ya sauka daga Naira 450 zuwa Naira 500 zuwa Naira 250 zuwa Naira 300.

Naman Sa kuwa ya ci gaba da kasancewa mai tsada tsakanin Naira 3,000 zuwa Naira 3,200 kowane kilo, yayin da farashin kaji ya sauka daga Naira 10,000 zuwa Naira 15,000 zuwa Naira 6,000.

Wani dillalin hatsi daga Sokoto, Adamu Isa, ya danganta saukar farashin da matakin da gwamnatin Jihar Akwa Ibom ta dauka na rusa kungiyoyin kasuwa a manyan kasuwanni.

Wani dillalin dabbobi, Abubakar Garba, ya bayyana cewa matakin Gwamnonin Nijeriya (NGF) na kawar da harajin kan tituna toll points “shima babban dalili ne da ya taimaka wajen rage farashin muhimman kayan masarufi.”

Farashi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Next Post

Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP

LABARAI MASU NASABA

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.