Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Jihar Kano sun gabatar da sunayen mutane uku ga gwamna Abba Kabir Yusuf domin duba su don cike gurbin mataimakin gwamna.
An gabatar da sunayen ne bayan wani taro da aka gudanar ranar Asabar, bayan shawarwari da aka yi tsakanin shugabannin jam’iyyar.
- NPA Ta Ƙuduri Aniyar Inganta Tashar Jiragen Ruwa Ta Apapa
- Kwankwasiyya Ta Kai Ƙorafi DSS Kan Zargin Cin Zarafin Kwankwaso A Shafukan Sada Zumunta
Taron ya gudana ne karkashin jagorancin tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, kuma ya samu halartar gwamna Abba Kabir Yusuf, mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin, Sanata Suleiman Abdulrahman Kawu Sumaila, da sauran masu ruwa da tsaki.
A karshen taron, an gabatar da sunayen tsohon kakakin majalisar dokokin Jihar Kano, Kabiru Alhassan Rurum; tsohon kwamishinan kananan hukumomi, Murtala Sule Garo; da kuma Rabiu Suleiman Bichi.
Gurbin ya zama babu kowa ne bayan murabus din tsohon mataimakin gwamna, Aminu Abdussalam Gwarzo, sakamakon barazanar tsige shi da majalisar dokokin Jihar Kano ta yi, bisa zargin aikata ba daidai ba.
ADVERTISEMENT















Discussion about this post