ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NPA Ta Ƙuduri Aniyar Inganta Tashar Jiragen Ruwa Ta Apapa

by Bello Hamza and Abubakar Sulaiman
3 months ago
NPA

Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Ƙasa NPA, ta nanata ƙudurin ta na cewa, ta na kan gudanar da shirye-shiyen zamantakewar da Tashar Jiragen Ruwa ta jihar Legas.

Ta ce, za ta gudanar da aikin ne, ta hanyar amfani da tsarin zamani na ƙasa ne NSW.

  • Manoma Da Dama Za Su Yi Watsi Da Fannin Noma A Taraba A 2026 -AFAN
  • Ko Ka San Manyan Ƴanwasa Da Ƙasashen Da Ba Za Su Je Gasar Cin Kofin Duniya Ba?

Shugaban hukumar Dakta Abubakar Ɗantsoho, ya bayyana haka a hirarsa da manema labarai a jihar Legas.

ADVERTISEMENT

Ɗantsoho ya bayyana haka ne, ta bakin Janar Manaja kuma mai samar da bayanai na hukumar Ikechukwu Onyemakara.

Shugaban ya ƙara da cewa, idan aka wanzar da tsarin na NSW a aikin Tashar ta jihar Legas, hakan zai taimaka matuƙa wajen magance abubuwa da dama da suka haɗa da, cunkoso da kuma samun jinkiri, wajen shigar da kaya zuwa cikin Tashar.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Da yake yin tsokaci kan taarin ETO na shigar manyan motoci cikin Tashar, shugaban ya bayyana cewa, a yanzu haka ana kan yin nazari a kansa kafin nan da, ƙare wa’adin kwangilarsa.

Ɗantsoho ya ci gaba da cewa, tsarin na ETO, an samar da shi ne, bisa nufin kawo ƙarshen ƙalubalen da ake fuskanta, musamman ga mazauna yankin Apapa, wajen shigar da kaya zuwa cikin Tashar ta jihar Legas.

Shugaban ya bayyana cewa, tsarin na ci gaba da taimaka wa matuƙa wajen ƙara inganta, ayyukan da ake gudanar wa, a Tashar da kuma magance sauran matsaloli, a Tashar.

“Bayan ƙarewar kwantiragin tsarin za mu sake yin nazari a kan kwantiragin,musamman, biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da aka bijoro da su bisa nufin ƙara inganta ayyukan Tashar, ” Inji Ɗantsoho.

“Za a gudanar da wannan nazarin ne, tare haɗaka da hukumar ta NPA da kuma ƙungiyar manyan motoci ta TTI inda daga bisani, za a gabatar da tsarin na ETO, ”

Kan batun tsarin tantance shigar da kaya zuwa cikin Tashar Jiragen Ruwan ta jihar Legas, shugaban ya bayyana cewa, abokan huɗɗa ne,za su bayar da shawarar da ta kamata, kan tsarin da za a yi amfani da shi.

Ɗantsoho ya ci gaba da cewa hukumar za ta kuma mayar da hankali wajen ganin ta ta ƙara inganta ayyukan shigar da kaya zuwa cikin Tashar ciki har da yin amfani da layin Dogo na shigar da kaya zuwa cikin Tashar ta jihar Legas.

Shugaban ya kuma bayyana jindaɗinsa kan manufar hukumar wanda ya ce, hatta manyan gobe, suma ba za a bar su a baya wajen amfana da manufufin ba.

Ɗantsoho ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ci gaba da bayar da gudunmawar su wajen sanya ido kan ayyukan ci gaba, da hukumar ke ci gaba da ƙirƙiro wa.

 

NPA
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
NPA
Abubakar Sulaiman
Website |  + posts Bio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
  • Abubakar Sulaiman
    Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Sabon Nau’in Zakara Na ‘MoorBeta’ Zai Ƙara Haɓaka Fannin Kiwon Kaji

Sabon Nau’in Zakara Na ‘MoorBeta’ Zai Ƙara Haɓaka Fannin Kiwon Kaji

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.