ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NPA Ta Ƙuduri Aniyar Inganta Tashar Jiragen Ruwa Ta Apapa

by Bello Hamza and Abubakar Sulaiman
2 months ago
NPA

Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Ƙasa NPA, ta nanata ƙudurin ta na cewa, ta na kan gudanar da shirye-shiyen zamantakewar da Tashar Jiragen Ruwa ta jihar Legas.

Ta ce, za ta gudanar da aikin ne, ta hanyar amfani da tsarin zamani na ƙasa ne NSW.

  • Manoma Da Dama Za Su Yi Watsi Da Fannin Noma A Taraba A 2026 -AFAN
  • Ko Ka San Manyan Ƴanwasa Da Ƙasashen Da Ba Za Su Je Gasar Cin Kofin Duniya Ba?

Shugaban hukumar Dakta Abubakar Ɗantsoho, ya bayyana haka a hirarsa da manema labarai a jihar Legas.

ADVERTISEMENT

Ɗantsoho ya bayyana haka ne, ta bakin Janar Manaja kuma mai samar da bayanai na hukumar Ikechukwu Onyemakara.

Shugaban ya ƙara da cewa, idan aka wanzar da tsarin na NSW a aikin Tashar ta jihar Legas, hakan zai taimaka matuƙa wajen magance abubuwa da dama da suka haɗa da, cunkoso da kuma samun jinkiri, wajen shigar da kaya zuwa cikin Tashar.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Da yake yin tsokaci kan taarin ETO na shigar manyan motoci cikin Tashar, shugaban ya bayyana cewa, a yanzu haka ana kan yin nazari a kansa kafin nan da, ƙare wa’adin kwangilarsa.

Ɗantsoho ya ci gaba da cewa, tsarin na ETO, an samar da shi ne, bisa nufin kawo ƙarshen ƙalubalen da ake fuskanta, musamman ga mazauna yankin Apapa, wajen shigar da kaya zuwa cikin Tashar ta jihar Legas.

Shugaban ya bayyana cewa, tsarin na ci gaba da taimaka wa matuƙa wajen ƙara inganta, ayyukan da ake gudanar wa, a Tashar da kuma magance sauran matsaloli, a Tashar.

“Bayan ƙarewar kwantiragin tsarin za mu sake yin nazari a kan kwantiragin,musamman, biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da aka bijoro da su bisa nufin ƙara inganta ayyukan Tashar, ” Inji Ɗantsoho.

“Za a gudanar da wannan nazarin ne, tare haɗaka da hukumar ta NPA da kuma ƙungiyar manyan motoci ta TTI inda daga bisani, za a gabatar da tsarin na ETO, ”

Kan batun tsarin tantance shigar da kaya zuwa cikin Tashar Jiragen Ruwan ta jihar Legas, shugaban ya bayyana cewa, abokan huɗɗa ne,za su bayar da shawarar da ta kamata, kan tsarin da za a yi amfani da shi.

Ɗantsoho ya ci gaba da cewa hukumar za ta kuma mayar da hankali wajen ganin ta ta ƙara inganta ayyukan shigar da kaya zuwa cikin Tashar ciki har da yin amfani da layin Dogo na shigar da kaya zuwa cikin Tashar ta jihar Legas.

Shugaban ya kuma bayyana jindaɗinsa kan manufar hukumar wanda ya ce, hatta manyan gobe, suma ba za a bar su a baya wajen amfana da manufufin ba.

Ɗantsoho ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ci gaba da bayar da gudunmawar su wajen sanya ido kan ayyukan ci gaba, da hukumar ke ci gaba da ƙirƙiro wa.

 

NPA
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
NPA
Abubakar Sulaiman
Website |  + posts Bio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Sabon Nau’in Zakara Na ‘MoorBeta’ Zai Ƙara Haɓaka Fannin Kiwon Kaji

Sabon Nau’in Zakara Na ‘MoorBeta’ Zai Ƙara Haɓaka Fannin Kiwon Kaji

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.