Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Jihar Kano sun sayi fom ɗin tsayawa takara ga Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Tsohon shugaban jam’iyyar na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ne ya miƙa fom ɗin ga gwamnan yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar ranar Alhamis, inda hakan ya zama tamkar amincewa da shi ne a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar a jihar.
Haka kuma, taron ya amince da Bola Ahmed Tinubu a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa guda ɗaya tilo na jam’iyyar. Sai dai shugabannin jam’iyyar sun yi watsi da batun bai wa sauran ƴan takara tikitin kai tsaye.
Sun jaddada cewa duk sauran muƙamai za a tantance su ne ta hanyar tsarin cikin gida na jam’iyya, musamman ta hanyar sulhu da fahimtar juna (consensus).
Da yake miƙa fom ɗin, Ganduje ya ce sun riga sun amince da Gwamna Yusuf a matsayin ɗan takarar gwamna karo na biyu, yana mai cewa matakin yana nufin cika alƙawarin da suka ɗauka a baya.
Haka kuma, an gabatar da ƙudirin amincewa da Tinubu daga Rabiu Sulaiman Bichi, wanda duk mahalarta taron suka goyi baya baki daya.















Discussion about this post