Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya soki gwamnatin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan abin da ya bayyana a matsayin ƙoƙarin kare yawan bashin da ƙasar ke ci gaba da ciyowa duk da matsin tattalin arziƙi da rashin tsaro da ƴan Nijeriya ke fuskanta.
Atiku ya mayar da martani ne ga kalaman fadar shugaban ƙasa da suka ce bashin Nijeriya bai kai na wasu ƙasashen Afirka ba. A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya fitar, Atiku ya ce gwamnati ba ta san halin da talakawa ke ciki ba.
Ya ce babu wata gwamnati mai hankali da za ta auna ci gaban tattalin arziƙi da yawan bashin da ƙasa ke bi, maimakon ta duba rayuwar jama’a, da tsaro, da samar da ayyukan yi da walwalar al’umma. Ya zargi gwamnatin da mayar da shugabanci tamkar aikin farfaganda yayin da rayuwar jama’a ke ƙara taɓarɓarewa.
“A lokacin da miliyoyin ƴan Nijeriya ba sa iya cin abinci sau daya a rana, iyaye na cire ƴaƴansu daga makaranta saboda tsadar rayuwa, kuma mutane na kasafin kuɗin fansa idan masu garkuwa da mutane sun kamma su kamar yadda ake shirya wa biyan kuɗin makaranta, gwamnati na murnar yawan bashin da ake bin Nijeriya,” in ji Atiku.
Atiku Abubakar ya kuma ce rashin tsaro ya ƙara tsananta, inda ya yi zargin cewa manoma ba sa iya zuwa gonakinsu saboda hare-haren ƴan bindiga da masu tayar da ƙayar baya. Ya buƙaci gwamnatin tarayya ta mayar da hankali wajen magance matsalolin tsaro da tattalin arziƙi maimakon dogaro da yaɗa farfaganda.














