Jagoran ɗarikar Kwankwasiyya kuma jigo a jam’iyyar NDC, Rabiu Musa Kwankwaso, ya sake mayar da martani ga gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, kan rikicin siyasar da ke tsakaninsu bayan rabuwar ƙawance da suka yi a bana.
Da yake jawabi ga magoya bayansa a gidansa da ke Miller Road a Kano ranar Laraba, Kwankwaso ya ce babu laifi idan ya kira wasu ‘yan siyasa “yaransa” a siyasa, yana mai cewa hatta tsohon gwamna Abdullahi Umar Ganduje wanda ya yi mataimakinsa na tsawon shekaru takwas ba zai iya musanta cewa ya taba zama yaronsa a siyasa ba.
“In ba rashin kunya ba ne, ta yaya Mai Gidan Ruwa ko Aminu Goro za su ce ba yarana ba ne a siyasa? Ta yaya ma Ganduje zai ce bai taba zama yarona ba?” in ji Rabiu Musa Kwankwaso.
Kalaman Kwankwaso sun zo ne bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nuna rashin jin daɗinsa kan yadda tsohon gwamnan ke kiransa “Abba PA” ko “Yaro,” duk da cewa yana da shekaru 63 a duniya. Gwamnan ya kuma gargaɗi Kwankwaso da ya mutunta kansa, yana mai cewa shiru shiru ba tsoro ba ne.
Tun bayan da gwamnan ya bar tafiyar Kwankwasiyya tare da sauya sheƙa daga NNPP zuwa APC, dangantaka tsakaninsa da Rabiu Musa Kwankwaso ke ci gaba da tsami, inda tsohon gwamnan ke zarginsa da cin amanar siyasa.














Discussion about this post