Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23
A yau Alhamis aka bude bikin baje koli na 23 na Sin da ASEAN da taron tattauna kasuwanci da zuba...
A yau Alhamis aka bude bikin baje koli na 23 na Sin da ASEAN da taron tattauna kasuwanci da zuba...
Gwamnatin yankin musammam na Hong Kong na kasar Sin, ta fitar da shirin raya tattalin arziki da zamantakewa na shekaru 5, a jiya Laraba. Wannan shi ne karo na farko da aka fitar da cikakken shiri domin raya tattalin arziki da zamantakewa a yankin na musammam na Hong Kong. Shirin na shekaru 5 ya alamta shigar yankin cikin fagen shugabancin al’umma mai mayar da hankali kan cikakken tsari mai hangen nesa da fada da cikawa. A matsayinsa na wurin da aka fi gudanar da harkokin tattalin arziki cikin ‘yancin a duniya, kuma cibiyar hada-hadar kudi ta duniya, Hong Kong ya zama wata muhimmiyar kasuwa mai tasiri a yankin kudu maso gabashin Asia da yammacin Asia da kudancin Amurka a shekarun baya-bayan nan. Jerin harkokin da suka shafi hada-hadar kudi da cinikayya da matakan kirkire-kirkire da aka zayyana cikin shirin na shekaru biyar-biyar na farko, zai kara karfafa matsayin Hong Kong na cibiyar hulda da hada-hada. Ana sa ran karkashin jagorancin shirin na shekaru biyar-biyar na farko, Hong Kong zai ci gaba da amfani da fifiko na musammam da yake da su na dogaro da babban yankin Sin da hadewa da sassan duniya, domin hawa sabon tafarkin shugabanci da samun wadata. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a wanzar da kwazo domin fadada, da karfafa ci gaban fannin kere-kere, ta yadda za a samar da goyon baya mai karfi ga bunkasa zamanantarwa irin ta kasar Sin. Shugaba Xi, wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana shugaban hukumar zartarwa ta rundunar sojojin kasar Sin, ya yi kiran ne cikin wani umarni da ya bayar a baya-bayan nan, wanda aka gabatar a yayin taron kasa kan batun bunkasa kere-kere, wanda ya gudana jiya Laraba da yau Alhamis a birnin Beijing. Shugaba Xi, ya ce ya kamata a kara azamar tabbatar da ci gaba mai inganci, da tsaro bisa matakin koli, da samar da ci gaba mai kunshe da basira kana marar gurbata yanayi, a kuma mayar da tsarin hada-hadar masana’antun kasar Sin mai karin dogaro da kai da juriyar hadurra. Daga nan sai shugaban na Sin ya jaddada bukatar gaggauta bunkasa zamanantar da tsarin ayyukan masana’antu ta hanyar ingiza kere-kere a matsayin kashin bayan hakan, da karfafa tushen sashen tattalin arziki mai nasaba da sarrafawa, da hada-hadar sayar da hajoji da hidimomi. (Saminu Alhassan)
Fasahar kirkirarriyar basira ta AI na ci gaba da fita daga dakunan bincike cikin sauri, tana shiga masana’antu, harkokin sufuri,...
Kasar Sin ta amince tare da fitar da jerin ka’idoji irinsa na 3, na na’urar kiwon lafiya mai sadarwa tsakanin...
A yau Laraba, kasar Sin ta harba taurarin dan’adam guda tara zuwa da’irorin da aka tsara hawansu a sararin samaniya...
Shugaban kasar Sin, Xi Jinping, ya aika da sakon taya murna ga Jami'ar Jilin wacce take bikin cika shekaru 80...
Tattalin arzikin kasar Sin ya ci gaba da tafiya a turba mai kyau a watan Agusta, inda ci gabansa ya...
An rufe bikin baje kolin hada-hadar ba da hidima ta kasa da kasa CIFTIS na shekara ta 2026 a ranar...
A jiya Litinin ne aka bude babban taro karo na 70, na hukumar lura da makamashin nukiliya ta kasa da kasa wato IAEA a birnin Vienna dake Austria. Da yake jawabi a yayin taron, shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Sin Shan Zhongde, ya ce amfani da makamashin nukiliya cikin lumana ya shafi jin dadin dukkan bil’adama, wanda hakan ya sa ya fi muhimmanci ga dukkan bangarorin su tsaya tsayin daka kan goyon bayan ra’ayin cudanyar bangarori daban-daban, da kuma kara zurfafa hadin kai tsakanin su. Shan ya kara da cewa, Sin ta dage wajen bunkasa makamashin nukiliya cikin tsari da tsaro, kuma ta daidaita ci gaban da ke da alaka da kirkire-kirkire da tsaro, da kuma gudanar da hadin gwiwa a bude. A nan gaba, Sin za ta mayar da hankali kan muhimman fannoni guda hudu, na farko shi ne daidaita ci gaba, da tsaro don fadada sabbin fannoni, da nufin yin hadin gwiwar makamashin nukiliya. Na biyu kuma, za ta tabbatar da dorewar ci gaba cikin tsaro, don kiyaye tsaron nukiliya na duniya. Na uku kuma, za a bi tsari mai amfanar da mutane, don inganta kimiyya da fasahar nukiliya, ta yadda za su kawo alherai ga jama’a. Kana na karshe, za a aiwatar da manyan tsare-tsare guda hudu na duniya, don inganta tsarin shugabancin duniya. (Safiyah Ma)
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.