ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Ba Neman Kuɗi Nake Yi Ba, Na Shiga Siyasa Ne Don Ceto Al’umma” – Tsohon Shugaban DSS

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Kuɗi

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Tsohon Darakta-Janar na Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS), Lawal Daura, ya bayyana cewa ba don neman riba ko kuɗi ya shiga siyasa ba, sai domin ceton rayuka da kuma kuɓutar da jihar Katsina daga matsalar rashin tsaro da ke addabarta. Daura ya yi wannan bayani ne a ranar Alhamis yayin taron sake haɗuwar Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Government College Funtua (FOBA), ajin 1969, inda ya samu goyon baya a kan burinsa na tsayawa takarar gwamna a zaɓen 2027.

Tsohon shugaban DSS ɗin ya bayyana kansa a matsayin “makanikin siyasa,” yana mai cewa shigarsa siyasa na nufin gyara matsalolin tsaro da suka addabi jihar. Ya ce, “Duk lokacin da ka ga makanike to da kayan aikinsa, ka san akwai matsala. Haƙiƙa, akwai matsala a jiharmu, kuma wannan na shafar mu duka.” Ya ƙara da cewa tsaro shi ne mabuɗin warware sauran matsaloli, domin idan ba a samu tsaro ba, ba za a iya magance sauran ƙalubale ba.

  • Shugabannin Ƙasashe Huɗu Da Amurka Ta Kama Amurka Ta Gurfanar Da shugaban Ɓenezuela Nicolas Maduro
  • DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

Daura ya yi kukan cewa kasuwanni da dama a jihar da a da suke aiki har da daddare, yanzu ba sa aiki ko da a rana saboda rashin tsaro. Ya ce noma, wanda shi ne ginshiƙin tattalin arziƙin Katsina da makwabtan jihohi, ya samu babban koma baya sakamakon hare-haren masu tayar da ƙayar baya. Ya jaddada cewa ba shugabanci ko mukami ne burinsa ba, domin matsayin da ya taɓa riƙewa ya fi na gwamna girma, kuma sunansa ya riga ya yi fice har a wajen Nijeriya

ADVERTISEMENT

A nasa ɓangaren, Shugaban FOBA, Dakta Aliyu Yahaya, ya ce ƙwarewar Daura a fannin tsaro na ba shi damar magance matsalar rashin tsaro cikin ƙanƙanin lokaci idan aka zaɓe shi. Yahaya ya kuma yi alƙawarin cewa kowane mamba na ƙungiyar zai samar masa da ɗaruruwan ƙuri’u idan ya samu tikitin tsayawa takara a ƙarƙashin kowace jam’iyyar siyasa.

Kuɗi
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
Kuɗi

Kotun Koli Ta Yi Watsi Da Ƙarar Kisan Kudirat Abiola, Ta Sallami Al-Mustapha

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.