Tsohon ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party, Yusuf Datti Baba-Ahmed, ya bayyana cewa yankin Arewa ba zai goyi bayan duk wata haɗaka tsakanin Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso ba gabanin zaɓen 2027. Ya kuma soki ficewar Obi daga jam’iyyar a lokacin da take fama da rikicin cikin gida.
Baba-Ahmed, wanda ya kasance abokin takarar Obi a zaben 2023, ya ce duk da kyakkyawar alaƙar da yake da su, akwai shakku kan yiwuwar haɗakar tasu ta samu karɓuwa a Arewa. Ya bayyana cewa shi ne ya taɓa ba Obi shawarar ya tuntuɓi Kwankwaso da wasu shugabannin adawa domin haɗa ƙarfi kafin zaɓen 2027.
Ya ce, “Abu ne mai wuya a ce Arewa za ta mara musu baya. Ko da yake ra’ayina ne ya kawo su tare, amma ko hakan zai yi tasiri kuwa, babban abin tambaya ne da lokaci zai amsa.” Ya kuma tambayi dalilin da ya sa Kwankwaso bai goyi bayan Obi a zaben 2023 ba, yana mai cewa akwai yiwuwar rikicin jagoranci a cikin haɗakar.
Game da ficewar Obi daga jam’iyyar Labour, Baba-Ahmed ya ce ya kamata tsohon gwamnan na Anambra ya tsaya ya magance matsalolin jam’iyyar maimakon ficewa. A cewarsa, shugaba dole ne ya kasance mai juriya da ƙarfin hali wajen tinkarar ƙalubale.
Ya ƙara da cewa siyasa na buƙatar tsayin daka da iya jayayya, yana mai gargaɗin cewa duk wanda ba zai iya tsayawa ya fuskanci matsaloli ba, bai kamata ya shiga siyasa ba, musamman a ƙasa mai sarƙaƙiya kamar Nijeriya.















Discussion about this post