Tsohon gwamnan Jihar Sokoto kuma sanata mai wakiltar Sokoto ta Kudu, Aminu Tambuwal, ya ce babu wani mutum ko ƙungiya da za ta iya murɗe sakamakon zaɓen 2027, yana mai jaddada cewa ‘yan Nijeriya ne za su yanke hukunci kan shugabannin da za su zaɓa.
Tambuwal ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai bayan taron zaɓen shugabannin jam’iyyar ADC a Jihar Sokoto, inda ya yi watsi da zargin cewa za a rubuta sakamakon zaɓen dai zai nuna APC ta yo nasara.
- Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan
- APC Ta Zaɓi Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Maye Gurbin Mataimakin Gwamna
Ya ce ba zai yiwu a yi nasara ta hanyar ƙirƙirar sakamako ba, yana mai tuna yadda a baya ya tsaya kan ra’ayinsa a lokuta daban-daban, ciki har da saɓaninsa da tsoffin shugabannin ƙasa kamar Goodluck Jonathan da Muhammadu Buhari.
Sanatan ya kuma danganta yawaitar sauya sheƙa zuwa APC da rashin tabbas a siyasa, yana mai cewa wasu gwamnoni na shiga jam’iyyar ne saboda tsoron yadda zaɓen 2027 zai kasance, ba wai don an samu ingantaccen shugabanci ba.
Ya ƙara da cewa babu yadda za a yi a yi amfani da hukumomin tsaro ko INEC wajen karkatar da sakamakon zaɓe, yana mai jaddada cewa ‘yan Nijeriya sun waye kuma za su kare haƙƙinsu.
Tambuwal ya yi alƙawarin cewa idan ADC ta karɓi mulki, za ta magance matsalar tsaro tare da farfaɗo da tattalin arziƙi, yana mai kira ga jama’a su haɗa kai domin cimma wannan buri a zaɓen 2027.















Discussion about this post