Yadda Kwankwaso Ya Rabauta Da Hannun iran#
Jagoran tafiyar Kwankwasiyya kuma tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce ɓangaren ya amince da karɓar kaso 60 cikin 100 a tsarin rabon iko da jam’iyyar (ADC), duk da cewa an ba su damar karɓar kaso 80. Ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi ga magoya bayansa a gidansa, a wani bidiyo da aka wallafa a Facebook.
- Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo
- Sin Ta Bukaci Amurka Da Isra’ila Da Iran Su Dakatar Da Yaki Nan Take
Kwankwaso ya ce sun ƙi karɓar kaso mafi yawa ne domin ƙarfafa haɗin kai da bai wa sauran ɓangarori damar shiga cikin tafiyar. A cewarsa, manufarsu ita ce haɗa kan jama’a da faɗaɗa sahun masu ruwa da tsaki a cikin kawancen siyasar.
Ya ƙara da cewa wannan tsari ya yi daidai da irin yarjejeniyoyin da suka yi a baya lokacin da suka sauya sheƙa daga jam’iyyar PDP)b zuwa All Progressives Congress (APC), inda suka yi amfani da tsarin rabon 60 da 40.
Tsohon gwamnan ya kuma bayyana yadda aka raba muƙamai a matakin ƙananan hukumomi, inda ya ce sun riƙe kujerun shugabanni 34 tare da bai wa abokan kawancensu 10, amma suka ci gaba da riƙe kujerun mataimakan shugabanni a waɗannan wurare domin daidaito.
A ƙarshe, ya buƙaci mambobin tafiyar Kwankwasiyya da su yi haƙuri wajen rabon muƙamai, yana mai gargaɗin su guji matsin lamba ko nacewa kan wasu mutane, yana mai cewa haƙuri da fahimta su ne mabuɗin nasara a irin wannan kawance.















Discussion about this post