Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Kano sun amince da Murtala Sule Garo a matsayin wanda suka fi so ya maye gurbin mataimakin gwamna.
Matakin ya biyo bayan sauyin siyasa a jihar, musamman bayan murabus ɗin tsohon mataimakin gwamna, Aminu Abdussalam Gwarzo, a ranar 27 ga Maris, 2026, da kuma ƙin sauya sheƙarsa tare da gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa APC.
- APC Ta Gabatar Da Mutane Uku Domin Cike Muƙamin Kujerar Mataimakin Gwamnan Kano
- Daga “yaro mai gyaran babur” zuwa zakaran duniya: Labarin nasarar Zhang Xue mai dogaro da karfin samar da kayayyaki na kasar Sin
Tun da farko, masu ruwa da tsakin sun gabatar da sunayen mutane uku ga gwamnan, ciki har da Sule Garo, da Rabiu Suleiman Bichi da kuma Alhassan Rurum, bisa la’akari da gogewa da gudunmawar da suka bayar.
Sai dai bayan dogon nazari, an amince da Murtala Sule Garo saboda ƙwarewarsa a siyasa ta ƙasa da kuma hidimarsa a matsayin shugaban ƙaramar hukuma, kwamishina da kuma shugaban Association of Local Governments of Nigeria (ALGON).
Majiyoyi sun ce za a gudanar da binciken tsaro da tantancewa kan wanda aka zaba a Abuja, kafin gwamna Yusuf ya tuntuɓi Bola Ahmed Tinubu, sannan ya miƙa sunan ga majalisar dokokin jihar domin tantancewa da amincewa bisa tanadin kundin tsarin mulki.















Discussion about this post