ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ba – Gwamna Lawal

by Leadership Hausa
3 years ago
Sulhu

Gwamnan Dauda Lawal na jihar Zamfara, ya jaddada aniyar gwamnatinsa na kauracewa duk wani batun sulhu da barayi a fadin Jihar Zamfara.

Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin da ya halarci taron wa’azi na mako-mako da aka saba gudanarwa a Gusau, inda ya hori Malaman Addini da su kasance masu riko da gaskiya.

  • Yadda Kwankwaso Da Abba Suka Jagoranci Auren Gatan Mutum 1,800 A Kano
  • Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari

Wata takardar sanarwar manema labarai da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta ce wannan taron wa’azin mako an kwashe shekaru ana gudanar da shi, kuma wannan shi ne karo na 1,179.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, gwamnan ya yi kira ga dukkanin shugabannin bangarorin al’umma da su kasance masu gaskiya a dukkanin al’amuransu, tare kuma da yawaita addu’ar wanzuwar zaman lafiya a Jihar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Gwamna Dauda Lawal, a yayin da yake jawabi a wurin taron wa’azin mako a Gusau, ya bayyana irin hatsarin da yake tattare da yin sulhu da ‘yan bindiga, inda ya ce, babu abin da sulhun zai haifar sai karin karfi a gare su, tare da ci gaba da jefa al’umma cikin hatsari.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

“Ya bayyana cewa dole ne a fuskanci gaskiya, domin kuwa wadannan lalatattun sun nuna cewa ba wai sulhun suke son yi da gaske ba, saboda sun kasance masu saba alkawari. Babu abin da ya rage face a durfafe su da karfin tsiya.

“Gwamna Lawal ya kuma yi kira ga shugabanni, sarakuna da malamai da su rika fadin gaskiya komi dacinta, ba tare da la’akari da wa ta shafa ba, komi dadi ko rashin dadinta.

“Ya yi kira ga shugabannin siyasa da al’umma da su muhimmanta lamarin tsaron jihar gaba da siyasa, domin zaman lafiyan Zamfara shi ne gaba da komi.”

Tun farko dai, a nashi lakcar, shugaban Kwamitin Zakka da Wakafi na Jihar Zamfara, Sheikh Ahmad Umar Kanoma, ya yi dogon jawabi a kan muhimmanci sulhu, inda ya kawo sharudan da addinin musulunci ya gindaya wurin yin sulhu, da kuma yanayin da bai yiwuwa a yi sulhu a addinance.

Sulhu
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Kasashe 10 Da Ke Kan Gaba A Mallakar Ma’adanin Gwal A Afirka

Kasashe 10 Da Ke Kan Gaba A Mallakar Ma’adanin Gwal A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.