Shugaban FIFA, Gianni Infantino, ya sake jaddada cewa ƙasar Iran za ta buga wasannin FIFA World Cup 2026 a Amurka kamar yadda aka tsara.
Infantino ya bayyana haka ne a ranar Alhamis yayin taron ƙoli na FIFA da aka gudanar a Vancouver, inda ya ce tun farko an tsara Iran za ta buga wasanninta a ƙasashen Kanada, da Mexico da Amurka, kuma wannan tsari zai tabbata.
Ya ce duk da rikice-rikicen siyasa da suka taso a Gabas ta Tsakiya, musamman bayan hare-haren da Amurka da Israel suka kai kan Iran, hakan ba zai hana ƙasar shiga gasar ba.
“Ina tabbatar muku cewa babu shakka Iran za ta halarci gasar cin kofin duniya ta 2026, kuma za ta buga wasa a Amurka,” in ji Infantino ga wakilan ƙasashe mambobin FIFA.
A gefe guda, jami’an ƙwallon ƙafa na Iran sun nemi a mayar da wasanninsu zuwa Mexico, amma shugaban FIFA ya ƙi amincewa da wannan bukata.
Haka kuma, wasu shawarwari na maye gurbin Iran da Italiya sun taso, amma gwamnatin Amurka ta yi watsi da hakan, inda Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio, ya tabbatar da cewa za a tarbi ‘yan wasan Iran cikin mutunci.















Discussion about this post