ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Bukatar Tada Hankali Kan Karuwar Farashin Mai – IPMAN Ga ‘Yan Nijeriya

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Farashin

Da yake tofa albarkacin bakinsa, shugaban kamfanin dillalan mai a Nijeriya (IPMAN), Abubakar Maigandi ya bukaci ‘yan Nijeriya da cewa ka da su tayar da hankulansu dangane da bayanin basuka da yawan kudin jigila, musamman kan harsashen karuwar farashin litar mai.

“Babu wani bukatar ‘yan Nijeriya su firgita kan batun kalubalen kudi da NNPCL ke ciki. Ba bakon abu ba ne a basuka a lamarin kasuwanci. Muna aiki tare da Typical wajen ganin an ci gaba da samar da mai ba tare da yankewa ba ga ‘yan Nijeriya.

  • Za A Ci Gaba Da Fuskantar Karancin Man Fetur – IPMAN
  • Tallafin Man Da Nijeriya Ke Biya Yanzu Ya Zarce Nb700 Duk Wata – IPMAN

“Idan akwai karin farashin litar mai, NNPCL za ta sanar, haka nan da wadatar samar da mai din dukka,” ya shaida.

ADVERTISEMENT

Da aka tambayeshi kan nawa ‘yan kasuwa ke sayar da litar mai sai ya ce, “Wadanda suka samu mai ta hannun NNPCL da ke sayarwa kan naira 650 zuwa 700 a lita guda, wadanda suke samu kuma daga hannun masu zaman kansu suna sayarwa ne a kan naira 920.”

Ya kuma ce wadanda suke daukowa daga Legas zuwa kamar Maiduguri da wasu wurare farashin litarsu na zarce naira 920.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

A Jihar Nasarawa, Neja da kuma Kogi ana sayar da litar mai ne a tsakanin naira 850 zuwa naira 1,100 daga ranar Litinin da ta gabata yayin da ‘yan jarida suka yi zagayen duba halin da ake ciki.

A jihohin Delta, Bayelsa, Kurus Ribas, Imo, Inugu da kuma Abiyaa mazauna sun tabbatar da cewa su ma suna sayen litar mai ne daga kan kudi naira 870 zuwa 1,000.

Shi kuma manajan kamfanin BBH Consulting, Barr. Ameh Madaki, ya shaida cewa gwamnatin Tinubu ta kasa iya tafiyar da harkokin mai yadda ya dace. Ya bukaci gwamnatin da ta tashi tsaye ta hanzarta daukan matakan da suka dace wajen shawo kan kalubalen da suka dabaibaye lamarin mai kafin lamarin ya fi karfinta.

Ya ce, muddin gwamnati ta bari farashin mai ya kara tashi a wannan lokaci, hakan ya nuna akwai sakaci da rashin damuwa da halin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

Farashin
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Maiduguri

Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.