Kwamitin Kula da Asusun Gwamnati na Majalisar Wakilai (PAC) ya ƙwato Naira miliyan 521.76 na harajin VAT da CBN ta gaza miƙa wa gwamnatin tarayya, a wani ɓangare na binciken da yake gudanarwa kan asarar kuɗaɗen shiga da bashin da hukumomi ke bin gwamnati.
Binciken ya mayar da hankali ne kan mu’amalolin da suka shafi tsarin biyan kuɗi na Remita, inda kwamitin ya gano cewa CBN ba ta miƙa VAT na miliyan 521,765,134.17 da aka tara daga kuɗaɗen da aka samu ta hanyar Remita tsakanin Nuwamban 2018 da Afrilun 2024 ba.
Bayan umarnin da kwamitin ya bayar, CBN ta tabbatar a wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan watan 7 ga Mayu, 2026 cewa ta miƙa dukkan kuɗaɗen zuwa asusun gwamnatin tarayya tare da gabatar da shaidar biyan kuɗin.
Shugaban kwamitin, Hon. Bamidele Salam, ya ce nasarar ƙwato kuɗin na nuna muhimmancin sa ido da majalisa ke yi wajen kare dukiyar jama’a. Ya ƙara da cewa har yanzu kwamitin na bibiyar wasu kudaden da suka haɗa da Naira biliyan 3.28 na wasu kuɗaɗen da ba a mayar ba da kuma bashin TSA da ya kai sama da Naira biliyan 29.72.














Discussion about this post