An shigar da wata sabuwar ƙara a kotu da ke neman a umarci INEC ta soke rajistar jam’iyyar NDC, lamarin da ya ƙara janyo ce-ce-ku-ce kan halaccin jam’iyyar da shugabancinta.
Masu ƙarar na ƙalubalantar wasu matakai da suka shafi tsarin shugabanci da gudanarwar jam’iyyar, suna masu zargin cewa an samu saɓawar dokoki da ƙa’idojin da suka shafi rajistar jam’iyyun siyasa.
Rahotanni sun nuna cewa rikice-rikicen cikin gida da suka shafi shugabanci da tsarin gudanarwa na daga cikin muhimman batutuwan da kotun za ta yi nazari a kai yayin sauraron karar.
Ana sa ran hukuncin kotu kan lamarin zai yi tasiri ga makomar jam’iyyar da kuma shirye-shiryenta na zaɓukan da ke tafe, yayin da INEC da sauran ɓangarorin da abin ya shafa ke jiran yadda shari’ar za ta kaya.














Discussion about this post