Dakarun rundunar haɗin gwuiwa ta Operation Savannah Shield sun kama mutane biyar da ake zargi da bai wa ‘yan bindiga da masu ta’addanci bayanai a wasu sum,amen tsaro da suka gudanar a Jihar Neja. Haka kuma, jami’an sun ƙwato na’urorin sadarwa, kuɗi da wasu kayayyaki da ake zargin suna da alaƙa da ayyukan ta’addanci.
A cewar wata sanarwa da Kyaftin Jamilu Muhammed Yahaya, muƙaddashin jami’in yaɗa labarai na rundunar, ya sanya wa hannu, dakarun sun kama mutum uku yayin sintiri a yankin Doro da ke Wawa a Ƙaramar Hukumar Borgu ranar 6 ga Yuni, 2026.
Binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargin na da alaƙa da wata ƙungiyar ‘yan bindiga da ke aiki a yankin Duru da ke kusa da Gandun Dajin Kainji.
An ƙwato wayoyin salula guda biyu, da na’urar MP3 mai ɗauke da saƙonnin farfaganda da tayar da zaune tsaye, da kuma kuɗi Naira 113,400 daga hannunsu. Haka zalika, saƙonnin da ke cikin na’urar sun yi iƙirarin sace wani mutum a Jihar Kaduna tare da karɓar kuɗin fansa Naira miliyan 60.
A wani sumame daban, dakarun Bataliya ta 221 sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da tattara bayanan sirri kan sansanin sojoji.
Bugu da ƙari, binciken wayar ɗaya daga cikin waɗanda aka kama ya gano hoton wani mutum da aka yanke wa kai mai ɗauke da kwanan wata 2 ga Mayu, 2026, lamarin da ke ƙara nuna yiwuwar alaƙarsu da ayyukan ta’addanci.
An kuma ƙwato wayar Android guda ɗaya, da wayar salula, da babur da kuɗi Naira 86,100. Rundunar ta ce nasarar kamen na nuna ƙudirin Operation Savannah Shield na rusa hanyoyin tallafa wa ‘yan bindiga da masu ta’addanci a yankin Arewa ta Tsakiya. C, ,,, c. ,.














Discussion about this post